ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Ne Duniya Ta Hana Sake Farfado Da Tsarin Amfani Da Karfin Soja Na Japan

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
FILE - A crowd walks to the US consulate to protest against Trump's policy towards Greenland in Nuuk, Greenland, Saturday, Jan. 17, 2026. (AP Photo/Evgeniy Maloletka, File)

FILE - A crowd walks to the US consulate to protest against Trump's policy towards Greenland in Nuuk, Greenland, Saturday, Jan. 17, 2026. (AP Photo/Evgeniy Maloletka, File)

A farkon watan Nuwambar bara, Firaministar Japan Sanae Takaichi ta yi ikirari a bainar jama’a lokacin wani zaman majalisar dokokin kasar cewa, abin da ake kira da “makomar Taiwan” na iya zama wani “yanayi mai barazana ga dorewa” wanda zai ba Japan damar amfani da ‘yancin kare kai na gaba daya.

Wannan shi ne karo na farko tun bayan kayar da Japan a shekarar 1945 da wani shugaban kasar mai ci ya gabatar da ra’ayi a hukumance na cewa “makomar Taiwan wani lamari ne da zai iya shafar makomar Japan” yayin da yake danganta hakan da amfani da ‘yancin kare kai na gaba daya. Wannan kuma shi ne karo na farko da Japan ta bayyana burinta na tsoma baki bisa amfani da karfin soji a kan batun Taiwan, kuma karo na farko da Japan ta yi barazanar tilasta wa kasar Sin.

A tarihi, lokacin da take neman fadada kasarta, masu ra’ayin amfani da karfin soja na Japan sun rika nuna Japan a matsayin kasar da aka zalunta wacce ba ta da wani zabi, suna karkatar da gaskiya don neman goyon baya a cikin gida. Yanayi na bayar da dama sai suka kaddamar da yake-yake ba tare da la’akari da abokan hamayya ba, ko mummunan sakamako, ko sanarwa, ko kuma hanyoyin da za a yi amfani da su. Tunanin amfani da karfin soja yana ci gaba da ba da damar yin kalamai da ayyuka na ganganci ga shugabannin Japan na yanzu.

ADVERTISEMENT

Tsarin Japan na amfani da karfin soji ya haifar da yake-yake na zalunci na kasar kuma ya kasance tushen akidar masu tsattsauran ra’ayi na kasar.

Katobara da wasu ayyuka na Takaichi da sauransu ba abubuwa ne da suka zamo daban da na baya ba ta kowace fuska. A cikin ‘yan shekarun nan, Japan ta kara yawan kudin da take kashewa na tsaro har na tsawon shekaru 13 a jere, ta sassauta takunkumi kan aiwatar da manufar tsaron kai ta gaba daya, sannan sau da yawa ta sassauta dokar hana fitar da makamai, kana tana yunkurin aiki da abin da aka kira da “karfin dakile kawo hari,” har ma ta nemi yin gyara ga ka’idoji uku da ba su shafi sha’anin nukiliya ba.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Kudurin amfani da karfin soji na Japan hadari ne na gaske kuma mai bukatar matakin gaggawa. Idan Japan ta ci gaba da bin wannan muguwar hanya, duk kasashe da al’ummomin da suka himmatu ga tabbatar da adalci suna da ‘yancin sake duba miyagun laifukan Japan na tarihi da kuma sauke alhakin hana sake farfado da tsarin amfani da karfin soja. Wannan babban batu ne ga al’ummomin duniya wajen kare tsarin kasa da kasa da aka samar bayan yakin duiya na biyu da kuma gwaji na hakika don gano ko ita kanta Japan za ta iya ci gaba da raya zaman lafiya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Japan
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Japan
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Wazirin Ningi Ya Yi Murabus Bisa Zargin Shigar Da Siyasa Cikin Harƙoƙin Masarautar 

Wazirin Ningi Ya Yi Murabus Bisa Zargin Shigar Da Siyasa Cikin Harƙoƙin Masarautar 

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.