ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Ne Duniya Ta Hana Sake Farfado Da Tsarin Amfani Da Karfin Soja Na Japan

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
FILE - A crowd walks to the US consulate to protest against Trump's policy towards Greenland in Nuuk, Greenland, Saturday, Jan. 17, 2026. (AP Photo/Evgeniy Maloletka, File)

FILE - A crowd walks to the US consulate to protest against Trump's policy towards Greenland in Nuuk, Greenland, Saturday, Jan. 17, 2026. (AP Photo/Evgeniy Maloletka, File)

A farkon watan Nuwambar bara, Firaministar Japan Sanae Takaichi ta yi ikirari a bainar jama’a lokacin wani zaman majalisar dokokin kasar cewa, abin da ake kira da “makomar Taiwan” na iya zama wani “yanayi mai barazana ga dorewa” wanda zai ba Japan damar amfani da ‘yancin kare kai na gaba daya.

Wannan shi ne karo na farko tun bayan kayar da Japan a shekarar 1945 da wani shugaban kasar mai ci ya gabatar da ra’ayi a hukumance na cewa “makomar Taiwan wani lamari ne da zai iya shafar makomar Japan” yayin da yake danganta hakan da amfani da ‘yancin kare kai na gaba daya. Wannan kuma shi ne karo na farko da Japan ta bayyana burinta na tsoma baki bisa amfani da karfin soji a kan batun Taiwan, kuma karo na farko da Japan ta yi barazanar tilasta wa kasar Sin.

A tarihi, lokacin da take neman fadada kasarta, masu ra’ayin amfani da karfin soja na Japan sun rika nuna Japan a matsayin kasar da aka zalunta wacce ba ta da wani zabi, suna karkatar da gaskiya don neman goyon baya a cikin gida. Yanayi na bayar da dama sai suka kaddamar da yake-yake ba tare da la’akari da abokan hamayya ba, ko mummunan sakamako, ko sanarwa, ko kuma hanyoyin da za a yi amfani da su. Tunanin amfani da karfin soja yana ci gaba da ba da damar yin kalamai da ayyuka na ganganci ga shugabannin Japan na yanzu.

ADVERTISEMENT

Tsarin Japan na amfani da karfin soji ya haifar da yake-yake na zalunci na kasar kuma ya kasance tushen akidar masu tsattsauran ra’ayi na kasar.

Katobara da wasu ayyuka na Takaichi da sauransu ba abubuwa ne da suka zamo daban da na baya ba ta kowace fuska. A cikin ‘yan shekarun nan, Japan ta kara yawan kudin da take kashewa na tsaro har na tsawon shekaru 13 a jere, ta sassauta takunkumi kan aiwatar da manufar tsaron kai ta gaba daya, sannan sau da yawa ta sassauta dokar hana fitar da makamai, kana tana yunkurin aiki da abin da aka kira da “karfin dakile kawo hari,” har ma ta nemi yin gyara ga ka’idoji uku da ba su shafi sha’anin nukiliya ba.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Kudurin amfani da karfin soji na Japan hadari ne na gaske kuma mai bukatar matakin gaggawa. Idan Japan ta ci gaba da bin wannan muguwar hanya, duk kasashe da al’ummomin da suka himmatu ga tabbatar da adalci suna da ‘yancin sake duba miyagun laifukan Japan na tarihi da kuma sauke alhakin hana sake farfado da tsarin amfani da karfin soja. Wannan babban batu ne ga al’ummomin duniya wajen kare tsarin kasa da kasa da aka samar bayan yakin duiya na biyu da kuma gwaji na hakika don gano ko ita kanta Japan za ta iya ci gaba da raya zaman lafiya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Japan
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Japan
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina Kasa

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Wazirin Ningi Ya Yi Murabus Bisa Zargin Shigar Da Siyasa Cikin Harƙoƙin Masarautar 

Wazirin Ningi Ya Yi Murabus Bisa Zargin Shigar Da Siyasa Cikin Harƙoƙin Masarautar 

LABARAI MASU NASABA

Japan

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Japan

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.