ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wazirin Ningi Ya Yi Murabus Bisa Zargin Shigar Da Siyasa Cikin Harƙoƙin Masarautar 

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
4 months ago
Ningi

Wazirin Masarautar Ningi, Babban Ɗan Majalisa (Senior Councillor), kuma Shugaban Masu Zaɓen Sarki na Majalisar Masarautar Ningi, Amb. Shuaibu Ahmed Adamu ya yi murabus daga muƙaminsa. 

 

A cikin wata wasiƙa da tsohon Wazirin ya aike wa Sarkin Ningi, Alh. Haruna Yunusa M. Danyaya Mai kwanan wata 26 ga watan Janairun 2026 da wakilinmu ya ci karo da ita a ranar Alhamis, Ahmed ya ce, ya ɗauki matakin ne bisa zargin da ya yi na cewa siyasa ta shigo cikin harkokin gudanarwar Masarautar, musamman kan umarnin Gwamnatin Jihar Bauchi ta bayar wanda ya nemi a rage darajar matsayinsa na shugabancin masu zaɓen Sarkin masarautar.

ADVERTISEMENT
  • Za A Gudanar Da Dandalin Tattaunawa Na Masana Na Jam’iyyar JKS Da KMT A Birnin Beijing
  • Majalisar Dattawa Ta Kai Ta’aziyya Ga Al’ummar Kurmin Wali, Ta Yi Alkawarin Kayan Agaji

Wasiƙar na cewa: “Cikin cikakken girmamawa da matukar alhini, ina miƙa wannan wasiƙa domin sanar da Mai Martaba cewa na yanke shawarar yin murabus daga muƙamina na Wazirin Ningi, Babban Ɗan Majalisa (Senior Councillor), da kuma Shugaban Masu Zaɓen Sarki na Majalisar Masarautar Ningi, wanda zai fara aiki daga 26 ga Janairu, 2026.”

 

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

“Kusan tsawon shekaru hudu (4) ke nan da Allah Subhanahu Wa Taála, Ya ƙaddara Majalisar Masarautar Ningi, tare da amincewar Gwanatin Jihar Bauchi, ta tabbatar min da wannan babban muƙamin mai alfarma, na Wazirin Ningi.

 

“Tun da aka naɗa ni Waziri na riƙe muƙamin bilhaƙƙi da gaskiya, tare da cikakken sadaukarwa, da girmamawa al’adunmu na gargajiya. A matsayi na na Shugaban Masu Zaɓen Sarki, wanda wani nauyi ne da na riƙe cikin girmamawa da darajawa, na samu nasarar sauƙe nauyin jagorantar tsarin zaɓen Sarki cikin tsoron Allah, da kuma bin ƙa’idodin da doka ta tsayar.”

 

Ya ci gaba da cewa, “Shawara ta ta yin murabus daga matsayin Wazirin Ningi ba abu ne mai sauƙi ba ko kaɗan. Na yanke shawarar ne bayan dogon nazari da tunani kan abubuwan da suka faru kwanan nan yadda siyasa ta shigo cikin harkokin gudanarwar Masarautarmu, musamman kan umarnin da ya fito daga Gwamnatin Jihar Bauchi wanda ya nemi a rage darajar matsayina na Shugabancin Masu Zaɓen Sarki.

 

“Wannan umarnin ba sakamakon yarjejeniya ko buƙatar gudanarwar Majalisar Masarauta ba ne, illa dai sakamakon zagon-ƙasa na siyasa daga waje, ta hannun wasu da ke kusa da fadar Gwamnatin Jihar Bauchi.

 

“Abin takaici shi ne yadda Mai Girma Gwamna Sanata Bala Mohammed, ya gaggauta amincewa da burin wannan masu zagon-ƙasa, sannan ya umarci Mai Martaba da ku bayar da shawarar waɗannan canje-canjen,” in ji shi.

 

“Kan haka ne naga ba zan iya ci gaba da aiki na ba, ba tare da na saba wa ƙa’idodin da na rantse zan kare ba. Amincewa da wannan matsayi da aka rage wa daraja zai zama tamkar na yarda da sanya siyasa a cikin al’adun Masarauta,” ya nanata.

 

“Ina fata da gaske cewa tafiyata za ta zama sanadin yin tunani mai zurfi a cikin Majalisar Masarautar Ningi, da ma dukkan Masarautun dake faɗin Arewacin Nijeriya, tare da aika sako ga ‘yan siyasa masu son raunana tushen tarihinmu.”

 

“Na ji daɗin aiki ƙarƙashin Marigayi Sarki, Mai Martaba Alhaji Yunusa Muhammad Danyaya (Allah ya jikansa da rahama), sannan tun bayan naɗin ka, na ci gaba da aiki tuƙuru da sadaukar da kai ƙarƙashin ka, Mai Martaba Sarki Haruna. Har abada zan kasance mai godiya da irin yarda da kwarin gwiwar da Majalisar Masarauta, da kuma daukacin al’ummar Ningi suka ba ni.”

 

Ya nuna matukar godiya ga Allah (SWT) kan ɗimbin ni’imomin da ya yi masa, “Alhamdu Lillah, a tsawon lokacin da na yi ina Wazirin Ningi, na yi iyakacin ƙoƙari na wurin riƙe gaskiya da kauce wa zalunci.”

 

Ya nanata cewa zai ci gaba da kasancewa mai biyayya ga Masarauta da kishin al’ummar Ningi baki ɗaya.

 

“Ina rokon Allah Ya bamu zaman lafiya da ci gaban Masarautar Ningi da al’ummarta. Allah kuma Ya bawa Mai Martaba Sarki da Al’umar Masarautar Ningi hakuri kan wannan al’amari. Amin!”.

 

Amb. Shuaibu Ahmed Adamu ya kuma aike da kwafin wasiƙar ga Gwamnan Jihar Bauchi da Shugaban Hukumar Hidimar Ƙananan Hukumomi, Jihar Bauchi.

Ningi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba
Ningi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Binciken CGTN: Ya Kamata Hadin-Gwiwar Sin Da Birtaniya Ya Kara Taka Rawa

Binciken CGTN: Ya Kamata Hadin-Gwiwar Sin Da Birtaniya Ya Kara Taka Rawa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.