ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wazirin Ningi Ya Yi Murabus Bisa Zargin Shigar Da Siyasa Cikin Harƙoƙin Masarautar 

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
7 months ago
Ningi

Wazirin Masarautar Ningi, Babban Ɗan Majalisa (Senior Councillor), kuma Shugaban Masu Zaɓen Sarki na Majalisar Masarautar Ningi, Amb. Shuaibu Ahmed Adamu ya yi murabus daga muƙaminsa. 

 

A cikin wata wasiƙa da tsohon Wazirin ya aike wa Sarkin Ningi, Alh. Haruna Yunusa M. Danyaya Mai kwanan wata 26 ga watan Janairun 2026 da wakilinmu ya ci karo da ita a ranar Alhamis, Ahmed ya ce, ya ɗauki matakin ne bisa zargin da ya yi na cewa siyasa ta shigo cikin harkokin gudanarwar Masarautar, musamman kan umarnin Gwamnatin Jihar Bauchi ta bayar wanda ya nemi a rage darajar matsayinsa na shugabancin masu zaɓen Sarkin masarautar.

ADVERTISEMENT
  • Za A Gudanar Da Dandalin Tattaunawa Na Masana Na Jam’iyyar JKS Da KMT A Birnin Beijing
  • Majalisar Dattawa Ta Kai Ta’aziyya Ga Al’ummar Kurmin Wali, Ta Yi Alkawarin Kayan Agaji

Wasiƙar na cewa: “Cikin cikakken girmamawa da matukar alhini, ina miƙa wannan wasiƙa domin sanar da Mai Martaba cewa na yanke shawarar yin murabus daga muƙamina na Wazirin Ningi, Babban Ɗan Majalisa (Senior Councillor), da kuma Shugaban Masu Zaɓen Sarki na Majalisar Masarautar Ningi, wanda zai fara aiki daga 26 ga Janairu, 2026.”

 

LABARAI MASU NASABA

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

“Kusan tsawon shekaru hudu (4) ke nan da Allah Subhanahu Wa Taála, Ya ƙaddara Majalisar Masarautar Ningi, tare da amincewar Gwanatin Jihar Bauchi, ta tabbatar min da wannan babban muƙamin mai alfarma, na Wazirin Ningi.

 

“Tun da aka naɗa ni Waziri na riƙe muƙamin bilhaƙƙi da gaskiya, tare da cikakken sadaukarwa, da girmamawa al’adunmu na gargajiya. A matsayi na na Shugaban Masu Zaɓen Sarki, wanda wani nauyi ne da na riƙe cikin girmamawa da darajawa, na samu nasarar sauƙe nauyin jagorantar tsarin zaɓen Sarki cikin tsoron Allah, da kuma bin ƙa’idodin da doka ta tsayar.”

 

Ya ci gaba da cewa, “Shawara ta ta yin murabus daga matsayin Wazirin Ningi ba abu ne mai sauƙi ba ko kaɗan. Na yanke shawarar ne bayan dogon nazari da tunani kan abubuwan da suka faru kwanan nan yadda siyasa ta shigo cikin harkokin gudanarwar Masarautarmu, musamman kan umarnin da ya fito daga Gwamnatin Jihar Bauchi wanda ya nemi a rage darajar matsayina na Shugabancin Masu Zaɓen Sarki.

 

“Wannan umarnin ba sakamakon yarjejeniya ko buƙatar gudanarwar Majalisar Masarauta ba ne, illa dai sakamakon zagon-ƙasa na siyasa daga waje, ta hannun wasu da ke kusa da fadar Gwamnatin Jihar Bauchi.

 

“Abin takaici shi ne yadda Mai Girma Gwamna Sanata Bala Mohammed, ya gaggauta amincewa da burin wannan masu zagon-ƙasa, sannan ya umarci Mai Martaba da ku bayar da shawarar waɗannan canje-canjen,” in ji shi.

 

“Kan haka ne naga ba zan iya ci gaba da aiki na ba, ba tare da na saba wa ƙa’idodin da na rantse zan kare ba. Amincewa da wannan matsayi da aka rage wa daraja zai zama tamkar na yarda da sanya siyasa a cikin al’adun Masarauta,” ya nanata.

 

“Ina fata da gaske cewa tafiyata za ta zama sanadin yin tunani mai zurfi a cikin Majalisar Masarautar Ningi, da ma dukkan Masarautun dake faɗin Arewacin Nijeriya, tare da aika sako ga ‘yan siyasa masu son raunana tushen tarihinmu.”

 

“Na ji daɗin aiki ƙarƙashin Marigayi Sarki, Mai Martaba Alhaji Yunusa Muhammad Danyaya (Allah ya jikansa da rahama), sannan tun bayan naɗin ka, na ci gaba da aiki tuƙuru da sadaukar da kai ƙarƙashin ka, Mai Martaba Sarki Haruna. Har abada zan kasance mai godiya da irin yarda da kwarin gwiwar da Majalisar Masarauta, da kuma daukacin al’ummar Ningi suka ba ni.”

 

Ya nuna matukar godiya ga Allah (SWT) kan ɗimbin ni’imomin da ya yi masa, “Alhamdu Lillah, a tsawon lokacin da na yi ina Wazirin Ningi, na yi iyakacin ƙoƙari na wurin riƙe gaskiya da kauce wa zalunci.”

 

Ya nanata cewa zai ci gaba da kasancewa mai biyayya ga Masarauta da kishin al’ummar Ningi baki ɗaya.

 

“Ina rokon Allah Ya bamu zaman lafiya da ci gaban Masarautar Ningi da al’ummarta. Allah kuma Ya bawa Mai Martaba Sarki da Al’umar Masarautar Ningi hakuri kan wannan al’amari. Amin!”.

 

Amb. Shuaibu Ahmed Adamu ya kuma aike da kwafin wasiƙar ga Gwamnan Jihar Bauchi da Shugaban Hukumar Hidimar Ƙananan Hukumomi, Jihar Bauchi.

Ningi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
Ningi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Rahotonni

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara
Labarai

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Next Post
Binciken CGTN: Ya Kamata Hadin-Gwiwar Sin Da Birtaniya Ya Kara Taka Rawa

Binciken CGTN: Ya Kamata Hadin-Gwiwar Sin Da Birtaniya Ya Kara Taka Rawa

LABARAI MASU NASABA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.