ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wazirin Ningi Ya Yi Murabus Bisa Zargin Shigar Da Siyasa Cikin Harƙoƙin Masarautar 

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
6 months ago
Ningi

Wazirin Masarautar Ningi, Babban Ɗan Majalisa (Senior Councillor), kuma Shugaban Masu Zaɓen Sarki na Majalisar Masarautar Ningi, Amb. Shuaibu Ahmed Adamu ya yi murabus daga muƙaminsa. 

 

A cikin wata wasiƙa da tsohon Wazirin ya aike wa Sarkin Ningi, Alh. Haruna Yunusa M. Danyaya Mai kwanan wata 26 ga watan Janairun 2026 da wakilinmu ya ci karo da ita a ranar Alhamis, Ahmed ya ce, ya ɗauki matakin ne bisa zargin da ya yi na cewa siyasa ta shigo cikin harkokin gudanarwar Masarautar, musamman kan umarnin Gwamnatin Jihar Bauchi ta bayar wanda ya nemi a rage darajar matsayinsa na shugabancin masu zaɓen Sarkin masarautar.

ADVERTISEMENT
  • Za A Gudanar Da Dandalin Tattaunawa Na Masana Na Jam’iyyar JKS Da KMT A Birnin Beijing
  • Majalisar Dattawa Ta Kai Ta’aziyya Ga Al’ummar Kurmin Wali, Ta Yi Alkawarin Kayan Agaji

Wasiƙar na cewa: “Cikin cikakken girmamawa da matukar alhini, ina miƙa wannan wasiƙa domin sanar da Mai Martaba cewa na yanke shawarar yin murabus daga muƙamina na Wazirin Ningi, Babban Ɗan Majalisa (Senior Councillor), da kuma Shugaban Masu Zaɓen Sarki na Majalisar Masarautar Ningi, wanda zai fara aiki daga 26 ga Janairu, 2026.”

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

“Kusan tsawon shekaru hudu (4) ke nan da Allah Subhanahu Wa Taála, Ya ƙaddara Majalisar Masarautar Ningi, tare da amincewar Gwanatin Jihar Bauchi, ta tabbatar min da wannan babban muƙamin mai alfarma, na Wazirin Ningi.

 

“Tun da aka naɗa ni Waziri na riƙe muƙamin bilhaƙƙi da gaskiya, tare da cikakken sadaukarwa, da girmamawa al’adunmu na gargajiya. A matsayi na na Shugaban Masu Zaɓen Sarki, wanda wani nauyi ne da na riƙe cikin girmamawa da darajawa, na samu nasarar sauƙe nauyin jagorantar tsarin zaɓen Sarki cikin tsoron Allah, da kuma bin ƙa’idodin da doka ta tsayar.”

 

Ya ci gaba da cewa, “Shawara ta ta yin murabus daga matsayin Wazirin Ningi ba abu ne mai sauƙi ba ko kaɗan. Na yanke shawarar ne bayan dogon nazari da tunani kan abubuwan da suka faru kwanan nan yadda siyasa ta shigo cikin harkokin gudanarwar Masarautarmu, musamman kan umarnin da ya fito daga Gwamnatin Jihar Bauchi wanda ya nemi a rage darajar matsayina na Shugabancin Masu Zaɓen Sarki.

 

“Wannan umarnin ba sakamakon yarjejeniya ko buƙatar gudanarwar Majalisar Masarauta ba ne, illa dai sakamakon zagon-ƙasa na siyasa daga waje, ta hannun wasu da ke kusa da fadar Gwamnatin Jihar Bauchi.

 

“Abin takaici shi ne yadda Mai Girma Gwamna Sanata Bala Mohammed, ya gaggauta amincewa da burin wannan masu zagon-ƙasa, sannan ya umarci Mai Martaba da ku bayar da shawarar waɗannan canje-canjen,” in ji shi.

 

“Kan haka ne naga ba zan iya ci gaba da aiki na ba, ba tare da na saba wa ƙa’idodin da na rantse zan kare ba. Amincewa da wannan matsayi da aka rage wa daraja zai zama tamkar na yarda da sanya siyasa a cikin al’adun Masarauta,” ya nanata.

 

“Ina fata da gaske cewa tafiyata za ta zama sanadin yin tunani mai zurfi a cikin Majalisar Masarautar Ningi, da ma dukkan Masarautun dake faɗin Arewacin Nijeriya, tare da aika sako ga ‘yan siyasa masu son raunana tushen tarihinmu.”

 

“Na ji daɗin aiki ƙarƙashin Marigayi Sarki, Mai Martaba Alhaji Yunusa Muhammad Danyaya (Allah ya jikansa da rahama), sannan tun bayan naɗin ka, na ci gaba da aiki tuƙuru da sadaukar da kai ƙarƙashin ka, Mai Martaba Sarki Haruna. Har abada zan kasance mai godiya da irin yarda da kwarin gwiwar da Majalisar Masarauta, da kuma daukacin al’ummar Ningi suka ba ni.”

 

Ya nuna matukar godiya ga Allah (SWT) kan ɗimbin ni’imomin da ya yi masa, “Alhamdu Lillah, a tsawon lokacin da na yi ina Wazirin Ningi, na yi iyakacin ƙoƙari na wurin riƙe gaskiya da kauce wa zalunci.”

 

Ya nanata cewa zai ci gaba da kasancewa mai biyayya ga Masarauta da kishin al’ummar Ningi baki ɗaya.

 

“Ina rokon Allah Ya bamu zaman lafiya da ci gaban Masarautar Ningi da al’ummarta. Allah kuma Ya bawa Mai Martaba Sarki da Al’umar Masarautar Ningi hakuri kan wannan al’amari. Amin!”.

 

Amb. Shuaibu Ahmed Adamu ya kuma aike da kwafin wasiƙar ga Gwamnan Jihar Bauchi da Shugaban Hukumar Hidimar Ƙananan Hukumomi, Jihar Bauchi.

Ningi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
Ningi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
Next Post
Binciken CGTN: Ya Kamata Hadin-Gwiwar Sin Da Birtaniya Ya Kara Taka Rawa

Binciken CGTN: Ya Kamata Hadin-Gwiwar Sin Da Birtaniya Ya Kara Taka Rawa

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.