Rundunar sojojin Nijeriya da ke gudanar da aikin ‘Operation Hadin Kai’ ta bukaci mazauna yankin Arewa maso Gabas su kasance cikin shiri da taka-tsantsan yayin da Musulmi ke shirin gudanar da bukukuwan Eid-el-Kabir na shekarar 2026, tare da tabbatar da cewa an tanadi isassun matakan tsaro domin tabbatar da zaman lafiya a lokacin bukukuwan.
Jami’in yada labarai na Hedikwatar Rundunar Hadin Gwiwa ta Arewa maso Gabas, Operation HADIN KAI, Laftanar Kanal Sani Uba, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin.
Sanarwar ta mika sakon taya murna ga daukacin al’ummar Musulmi gabanin bikin Sallah da aka shirya gudanarwa ranar Laraba, 28 ga Mayu, 2026.
Rundunar ta bayyana cewa ta shirya tsaf domin samar da ingantaccen tsaro tun kafin fara bukukuwan, domin tabbatar da yanayi mai cike da zaman lafiya da tsaro ga kowa.
Ta kara da cewa kare rayuka da dukiyoyin al’umma a fadin yankin na daga cikin manyan abubuwan da ta sanya a gaba.
Sai dai rundunar ta gargadi jama’a kan yiwuwar barazanar tsaro a lokacin bukukuwan.















Discussion about this post