Ƴan bindiga sun sake tilasta wa mazauna ƙauyuka 26 a Ƙaramar Hukumar Sabon- Birni da ke Jihar Sakkwato biyan kuɗaɗen haraji domin tsira da rayukansu, wajen ba su damar zuwa gonakinsu.
Majiyoyi daga yankin a gabascin Sakkwato sun bayyana cewa barayin dajin sun bayar da wa’adin kwanaki uku tare da gargaɗin manoma da su guji zuwa gonakinsu har sai sun biya kuɗin da suka buƙata.
Lamarin ya biyo bayan shigowar daminar bana wanda hakan babban ƙalubale ne kuma babbar barazana ga noma wajen samar da wadataccen abinci a yankin, wanda al’ummar suka bayyana cewa ƴan bindigar sun yi alwashin kisa ko sace duk waɗanda suka saba wa umurninsu a yayin wa’adin.
Garuruwan da lamarin ya shafa sun haɗa da Garin- Faji, Cina Barka, Zululu, Ɗan- Gari, Garin- Maigayya, Gardi, Katsira, Garin Baushe, Sulmawa, Zakin- Ganga, Ɗan- Kware, Garje, Dogon -Faru, Son- Allah, Garin- Galadima, Kafchi, Matabaya, Garin- Labo, Zango, Kaifin- Aska, Tsauna -Dogo, Tudun- Wada, Rambaɗawa, Ga- Itace, Nasarawa da Garin Idi.
Ɗaya daga cikin mazauna yankin ya bayyana cewar umarnin ya haifar da tsoro a tsakanin manoma da ke shirin fara noman bana, yana cewa sun ce duk wanda aka kama yana noma, ko dai a kashe shi ko a sace shi, kuma ba zai samu ƴanci ba sai ya biya kuɗin fansa na naira 500,000. Ya ce tuni suka fara tattara kuɗaɗe domin biyan harajin.
Wani mazaunin ƙauyen Zululu wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce yana shirin zuwa gonarsa ranar Juma’a ne lokacin da ya ji labarin wannan umarni.
Ya bayyana cewa ƴan bindigar sun umarci mazauna yankin da su dakatar da duk wasu ayyukan noma na tsawon kwanaki uku har sai ƙauyukan da abin ya shafa sun biya harajin da ake ƙaƙaba masu.
A cewarsu, jami’an tsaro na ƙwace dabbobinsu, suna jaddada cewa ba za a yi wani aikin noma ba har sai an biya harajin da aka ƙaƙaba masu tare da cewa suna tsammanin sarakunan gargajiya da malaman addini za su haɗu su tattauna da barayin dajin domin sanin adadin kuɗin da kowane ƙauye zai biya.
Ya ce “Muna biyan kuɗi kafin mu fara noma, sannan wani lokaci bayan kowane watanni biyu ko uku sai su sake zuwa. Ko bayan mun biya yanzu, za su iya dawowa bayan kusan watanni uku su ce babu wanda zai girbi gero har sai an sake biyan wani haraji.















Discussion about this post