ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto and Sulaiman
2 hours ago
Bindiga

Ƴan bindiga sun sake tilasta wa mazauna ƙauyuka 26 a Ƙaramar Hukumar Sabon- Birni da ke Jihar Sakkwato biyan kuɗaɗen haraji domin tsira da rayukansu, wajen ba su damar zuwa gonakinsu.

Majiyoyi daga yankin a gabascin Sakkwato sun bayyana cewa barayin dajin sun bayar da wa’adin kwanaki uku tare da gargaɗin manoma da su guji zuwa gonakinsu har sai sun biya kuɗin da suka buƙata.

Lamarin ya biyo bayan shigowar daminar bana wanda hakan babban ƙalubale ne kuma babbar barazana ga noma wajen samar da wadataccen abinci a yankin, wanda al’ummar suka bayyana cewa ƴan bindigar sun yi alwashin kisa ko sace duk waɗanda suka saba wa umurninsu a yayin wa’adin.

ADVERTISEMENT

Garuruwan da lamarin ya shafa sun haɗa da Garin- Faji, Cina Barka, Zululu, Ɗan- Gari, Garin- Maigayya, Gardi, Katsira, Garin Baushe, Sulmawa, Zakin- Ganga, Ɗan- Kware, Garje, Dogon -Faru, Son- Allah, Garin- Galadima, Kafchi, Matabaya, Garin- Labo, Zango, Kaifin- Aska, Tsauna -Dogo, Tudun- Wada, Rambaɗawa, Ga- Itace, Nasarawa da Garin Idi.

Ɗaya daga cikin mazauna yankin ya bayyana cewar umarnin ya haifar da tsoro a tsakanin manoma da ke shirin fara noman bana, yana cewa sun ce duk wanda aka kama yana noma, ko dai a kashe shi ko a sace shi, kuma ba zai samu ƴanci ba sai ya biya kuɗin fansa na naira 500,000. Ya ce tuni suka fara tattara kuɗaɗe domin biyan harajin.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

Wani mazaunin ƙauyen Zululu wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce yana shirin zuwa gonarsa ranar Juma’a ne lokacin da ya ji labarin wannan umarni.

Ya bayyana cewa ƴan bindigar sun umarci mazauna yankin da su dakatar da duk wasu ayyukan noma na tsawon kwanaki uku har sai ƙauyukan da abin ya shafa sun biya harajin da ake ƙaƙaba masu.

A cewarsu, jami’an tsaro na ƙwace dabbobinsu, suna jaddada cewa ba za a yi wani aikin noma ba har sai an biya harajin da aka ƙaƙaba masu tare da cewa suna tsammanin sarakunan gargajiya da malaman addini za su haɗu su tattauna da barayin dajin domin sanin adadin kuɗin da kowane ƙauye zai biya.

Ya ce “Muna biyan kuɗi kafin mu fara noma, sannan wani lokaci bayan kowane watanni biyu ko uku sai su sake zuwa. Ko bayan mun biya yanzu, za su iya dawowa bayan kusan watanni uku su ce babu wanda zai girbi gero har sai an sake biyan wani haraji.

Bindiga
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ posts Bio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Zulum Ya Ƙaddamar Da Gidajen Ƴan Gudun Hijira 100 A Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Siyasar 2027: Yadda Ƴan Adawa Ke Ƙara Shiga Tsaka-mai-wuya
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Dimokuradiyyar Nijeriya A Shekara 27:Ba Yabo Ba Fallasa
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato
Bindiga
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu
  • Sulaiman
    Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai
  • Sulaiman
    A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
  • Sulaiman
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
Rahotonni

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
Next Post
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Zulum Ya Ƙaddamar Da Gidajen Ƴan Gudun Hijira 100 A Sakkwato

Zulum Ya Ƙaddamar Da Gidajen Ƴan Gudun Hijira 100 A Sakkwato

June 20, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga

Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.