A wani ƙiyasi na Majalisar Ɗinkin Duniya an bayyana cewa akwai kimanin mutane Biliyan ɗaya a duniya wato kashi 15 cikin ɗari na mutanen duniya na da nakasa a wani sashi na jikinsu, sai dai ba dukkan su ne ke bara ko gararamba a titi ba, akasarinsu na da rayuwar da suka dogara da ita ko ayyukan da suke yi na moriya. Kamar yadda wata ƙididdiga ta nuna cewa a Nijeriya akwai kimanin kashi bakwai cikin ɗari na yara da shekarunsu suka wuce biyar, da kuma kashi tara cikin ɗari na manya da shekarunsu suka wuce 60 waɗanda ke rayuwa cikin ƙunci da tagayyara saboda wata nakasa da suke fama da ita.
Kodayake a shekarar 2018 gwamnatin Nijeriya ta kafa wata doka da ta haramta nuna wa nakasassu, masu buƙata ta musamman, wariya da ƙyama, amma duk da haka ba ta canza zani ba. A mu’amala ta yau da gobe, a makarantu da wuraren ayyuka, wani lokaci har ma a wuraren ibada. Akwai wasu abubuwa da dama da ake ganin bai dace a ga mai nakasa a wajen ba, ko kuma shi matsayinsa bai dace da wajen ba!
Muhammad Hussaini Yakubu, wani matashi ne da ya fuskanci wani ƙalubale na janye sunansa cikin wasu ɗalibai ƴan asalin Jihar Bauchi wanda gwamnatin baya ta yi wa alƙawarin ba su aiki, da zarar sun kammala karatunsu na digiri da suke yi a bangaren kimiyya da fasaha. Amma bayan ya samu wani tsautsayi a ɗakin binciken kimiyya na jami’ar da yake karatu, wanda a dalilin haka idanunsa suka tsiyaye, ya zama makaho, sai ya canza fannin karatun da yake yi zuwa sashin nazarin aikin jarida. Wannan ya jawo aka janye batun aikin da aka yi masa alƙawari, wanda a baya har ana biyansa wani alawus daga tallafin karatun da gwamnati take ba su. Rayuwa ta yi wa Muhammad ƙunci sosai, karatun ma ya nemi ya gagara, saboda ga lalurar makanta kuma ga rashin tallafin da zai biya kuɗin makaranta.
Kodayake bayan sanya baki da taimakon wasu ƴan’uwa an samu dai sabuwar gwamnatin Jihar Bauchi ta dawo masa da alƙawarin aikinsa, kuma har ya kammala karatun da yake yi. Amma ba kowa ne yake samun irin wannan gata ba, matasa da dama ba sa samun aikin yi, saboda wata nakasa da suke da ita, ana ganin ba za su iya ba. A dalilin haka da dama ke faɗawa mugun hannu, ko su shiga aikata munanan ayyuka, irinsu barace-barace, shaye-shaye, da wasu ayyukan da basu dace ba.
Ƙoƙarin da Gwamnonin wasu jihohi suka yi na kafa hukumomin kula da haƙƙoƙin nakasassu da sanya wasu masu iliminsu cikin harkokin gwamnati, ya taimaka wajen ɗaga darajar su da ƙara ba su bakin magana, a inda suka ga ana nuna musu wariya da bambanci. Kodayake wasu daga cikin mambobin waɗannan hukumomi na kokawa da rashin ba su muhimmancin da ya kamata daga bangaren gwamnati.
Na so in ji daga bakin Babban Sakataren Hukumar Kula da Nakasassu ta Ƙasa, James Lalu, dangane da abin da hukumar sa ke yi wajen isar da koke-koken masu buƙata ta musamman da a lokuta da dama suke ƙorafin ana hana musu damar cin wata moriya ta gwamnati a matsayinsu na ƴan ƙasa, duk da ilimi ko cancantar da suke da ita. Amma har kawo lokacin haɗa wannan rubutu bai waiwayi saƙona ba, duk kuwa da amsa min da ya yi na cewa ya ga saƙona.
Muna kira ga hukumomin gwamnati su ƙara sa ido kan yadda ake watsi da buƙatun nakasassu, da tauye musu damar da dokokin ƙasa suka basu a matsayinsu na ƴan ƙasa. A samar musu da tallafin lafiya da na ilimi, a inganta karatun ƴaƴansu, a koyar da su sana’o’in dogaro da kai, don hana su yawon bara, kuma a riƙa shigar da su cikin ayyukan raya ƙasa na gwamnati.
A yayin tattaunawar da aka yi, an tattauna game da buƙatar hukumomi da masu faɗa a ji su tallafawa masu buƙata ta musamman wajen shigar da su cikin ayyukan raya ƙasa, musamman abin da ya shafi samar musu da ayyukan yi da za su dogara da kansu ba tare da sun yi bara ko sun jingina da wani ba. Masu takardun shaidar karatu kuma a sama musu ayyukan yi da suka dace da lalurar da suke fama da ita. Ƙananan yara masu nakasa kuma a samar musu da tallafin karatu, da kayan koyon karatu da koyarwa ga malamai da ɗalibai, da suka dace da zamani. A kuma kula da batun lafiyarsu, musamman sun buƙaci a basu tallafi a bangaren kiwon lafiya ta hanyar inshora, yadda za su riƙa samun magunguna cikin sauƙi da rahusa.
Da wuya ka je wata ƙasa a duniya da ba za ka ga mabarata a titi ko a wasu kebantattun wurare suna bara ba, wasu don neman abin da za su ci a dalilin talauci da rashin gata, ko kuma don neman tallafin rayuwa saboda wata nakasa da ke tare da su. Duk kuwa da cewa a wasu ƙasashen gwamnatocin su na da wasu tsare tsare na tallafawa irin waɗannan mutane marasa gata da masu nakasa, da kuma kafa dokar hana bara a titi.














