Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC), ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta amince da manyan sauye-sauyen yi wa masu yi wa ƙasa hidima (NYSC).
Ministan Matasa, Ayodele Olawande, ya ce an yi waɗannan sauye-sauyen ne domin mayar da shirin ya fi mayar da hankali kan koyar da sana’o’i, kasuwanci, fasahar zamani da samar da damar aiki ga matasa.
Sabbin sauye-sauyen sun haɗa da amfani da fasaha wajen kiran masu yi wa ƙasa hidima, inganta tsaron wuraren da za a tura su, da kuma sake fasalin horon makonni shida da ake yi a sansanonin NYSC, inda za a fi koyar da shugabanci, fasahar zamani da harkokin kasuwanci.
Haka kuma, za a riƙa tura masu yi wa ƙasa hidima wuraren aiki da suka dace da fannin karatunsu da burin abin da suke son koya.
Gwamnati ta kuma ce za ta inganta sansanonin NYSC, ta ƙaddamar da sabon bikin kammala hidimar, tare da sake fasalin kayan NYSC domin ƙara inganta ƙwarewa da kishin ƙasa.
Domin aiwatar da sauye-sauyen, an umarci Babban Lauyan Tarayya da Ma’aikatar Matasa su gyara dokar NYSC da sauran dokokin da suka dace.
Gwamnatin ta ce waɗannan sauye-sauyen za su taimaka wajen shirya matasan Nijeriya domin fuskantar buƙatun tattalin arziƙin ƙasa tare da ƙara dacewar shirin NYSC da zamani.














