Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kashe mutane biyu tare da sace wasu biyar, ciki har da wata mai juna biyu, a harin da suka kai ƙauyen Rafin Ciyawa da ke Ƙaramar Hukumar Ningi a Jihar Bauchi.
Masanin harkokin tsaro Bakatsine ne, ya bayyana hakan a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Litinin.
Ya ce maharan sun kai harin ne a daren ranar Lahadi, inda suka kashe mutum biyu tare da yin garkuwa da wata mai juna biyu da wasu maza huɗu.
Mutane huɗu kuma sun jikkata a yayin harin.
An sallami mutum biyu daga asibiti bayan sun samu sauƙi, yayin da sauran biyun ke ci gaba da karɓar magani a wani asibiti da ke Bauchi sakamakon raunukan harbin bindiga.
Bakatsine ya ce hukumomin da abin ya shafa sun tabbatar da faruwar harin, kuma suna ɗaukar matakan da suka dace.
Lamarin ya jefa iyalan waɗanda aka sace cikin damuwa, yayin da suke fatan a ceto su, musamman mai juna biyu da ke cikin waɗanda aka yi garkuwa da su.














