Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta sanar a yau cewa, bisa gayyatar gwamnatin kasar Sin, firaministan jamhuriyar Uzbekistan Abdulla Aripov zai ziyarci kasar daga ranar 6 zuwa 7 ga wata.
A cewar sanarwar, Abdulla Aripov zai kuma jagoranci taron kwamitin hadin gwiwa na gwamnatocin Sin da Uzbekistan karo na 8, tare da mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS kuma mataimakin firaministan Sin Liu Guozhong. (Fa’iza Mustapha)
ADVERTISEMENT















Discussion about this post