ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gaskiya Ba Ta Buya…

by CMG Hausa
4 years ago
Gaskiya

Bisa ga dukkan alamu, ci gaban da kasar Sin ta samu a fannoni daban-daban da irin gudummawar da take bayarwa ga ci gaban zaman lafiya da kwanciyar hankali da bunkasuwar tattalin arziki da sauran sassan rayuwa a fadin duniya, ya damu wasu kasashe, wadanda suke kallo kansu a matsayin jagororin duniya.

Wannan ya sa daga lokaci zuwa lokaci, irin wadannan kasashe suke neman bata sunan kasar Sin ko salon jagorancin kasar da al’ummar kasar suka yi na’am da shi ko wani tsari da ta gabatar da nufin inganta rayuwar daukacin bil-Adama, kamar shawarar ziri daya da hanya daya da makamantansu.

  • Akwai Alamun Ba Gudu Ba Ja Da Baya A Kan Batun Taiwan

A wasu lokuta ma, irin wadannan kasashe dake adawa da ci gaban kasar Sin, kan fake da batutuwan tsarin demokiradiya da hakkin dan-Adam wajen neman tsoma baki a harkokin cikin gidan kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Sai dai, yanzu kan mage ya waye, kasashe da dama sun fahimci makircin kasashen yamma, inda suka fara dawowa daga rakiyarsu, domin kada su zuba musu kasa a cikin kununsu. Ta hanyar lalata shirye-shirye masu fa’ida da Sin din ta gabatar, da galibin kasashe masu tasowa suka amfana da su.

Na baya-bayan shi ne ministan kudi na kasar Bangladesh, inda ya fito kara ya soki wasu rahotannin karya da kafofin yada labaran Burtaniya suka yi kan kasar Sin, matakin dake nuna irin cikakkiyar amincewa da juna dake tsakanin Sin da Bangladesh, kuma hakan ya tabbatar da abin da kasar Sin ta sha fada cewa, gaskiya ba ta buya, kuma komin dadewa, adalci zai bayyana kansa.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

A matsayinta na kasa mai tasowa mafi girma a duniya, har kullum kasar Sin tana tare da sauran kasashe masu tasowa, kana tana gudanar da hadin gwiwar “ziri daya da hanya daya” da masu neman hana ruwa gudu ke neman batawa bisa tsarin tuntubar juna, da gudummawar hadin gwiwa, da samun moriyar juna.
Bayanai sun tabbatar da cewa, batun “tarkon bashi na kasar Sin” a zahiri wani “tarkon tattaunawa ne” da wasu mutane masu mugun nufi suka kirkira, don kawo cikas da kuma gurgunta hadin gwiwar moriyar juna tsakanin Sin da sauran kasashe masu tasowa.

Amma yanzu kan gaskiya ta bayyana, babu wanda zai rudi kasashen da suka amfana da tallafi da goyon bayan da kasar Sin ke baiwa abokanta kasashe masu tasowa.

Sanin kowa ne cewa, shawarar ziri daya da hanya daya, ta samu gagarumin goyon baya da shigar kasashe masu tasowa da dama.

Haka kuma hadin gwiwar ta haifar da kyakkyawan sakamako, ta kuma samar da fa’ida ta hakika ga jama’ar dukkan kasashe.

Don haka, duk wasu kalamai marasa kyau da ke neman bata sunan shawarar da hadin gwiwar Sin da sauran kasashe masu tasowa, da masu neman mayar da hannu agogo baya ke kirkira, kaikayi ne zai koma kan mashekiya. (Ibrahim Yaya)

Gaskiya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani
Daga Birnin Sin

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026
Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK
Daga Birnin Sin

Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

July 11, 2026
Next Post
Yanayin Kare Hakkin Dan Adam Na ‘Yan Kananan Kabilun Sin Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

Yanayin Kare Hakkin Dan Adam Na ‘Yan Kananan Kabilun Sin Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

July 11, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.