ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

GDP A Nijeriya Ya Taba Zarce Na China Da Malaysia Lokacin Da Muka Yi Watsi Da IMF — Gbenga Hashim

by Bello Hamza
5 months ago
GDP

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Dr. Gbenga Hashim, ya soki yadda Najeriya ke ci gaba da dogaro da shawarwarin tattalin arziki na Asusun Ba da Lamuni na Duniya (IMF), yana mai cewa durkushewar tattalin arzikin kasar ta samo asali ne daga manufofin da cibiyoyin waje suka tsara maimakon wadanda suka dace da yanayin cikin gida.

Hashim ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin wata hira da aka yi da shi a shirin ARISE TV na karfe 8 na dare, inda ya tattauna kan tattalin arzikin Najeriya, ci gaban kasa, da kuma shirin sa na gina tattalin arziki da darajarsa za ta kai dala tiriliyan 4.

  • Wani Mutum Ya Rasu Yayin Ciro Tukunyar Gas Daga Cikin Rijiya A Kano
  • Budurwa Ta Tsere Da Motar Saurayinta Bayan Sun Kwana A Otel A Abuja

A cewarsa, Najeriya ta fi yin nasara lokacin da take aiwatar da manufofin tattalin arziki masu cin gashin kai, yana mai kawo misalin matsayin tattalin arzikin kasar a shekarun 1970.

ADVERTISEMENT

“Lokacin da Najeriya ba ta bin IMF gaba daya ba, GDP a 1976 ya ninka na China sau uku, haka kuma GDP dinmu ya ninka na Malaysia sau biyu a 1966,” in ji shi.

GDP dai wani alama ne da masana tattalin arzikin k’asashe ke la’akari da shi wajen auna arzikin k’asa.

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Hashim ya kara da cewa, “Babu wata kasa mai muhimmanci da ke hadiye duk magungunan da IMF ke bayarwa.” Ya jaddada cewa IMF ba mai zuba jari ba ce, don haka hasashenta bai kamata ya zama babban ma’aunin ci gaban kasa ba.

Hashim ya ce ainihin ma’aunin nasarar tattalin arziki shi ne yadda rayuwar al’umma take inganta, ba wai alkaluman ci gaba kadai ba.

Dan takarar na PDP ya kuma yi watsi da murnar da Gwamnatin Tarayya ke yi kan ci gaban GDP na kashi hudu, yana mai cewa hakan bai isa ba idan aka yi la’akari da asarar tattalin arziki da aka samu a ‘yan shekarun nan.

“Bayan an rage GDP da kusan kashi 50, ci gaban kashi hudu har yanzu yana nuna koma baya. GDP ya ragu daga dala biliyan 574 a 2014 zuwa dala biliyan 230 a yanzu,” in ji shi, yana mai cewa gwamnatin All Progressives Congress (APC) ba za ta iya ikirarin samun ci gaba ba har sai tattalin arzikin Najeriya ya zarce matakin da ta gada a 2015.

Ya kwatanta hakan da zamanin tsohon Shugaba Olusegun Obasanjo, inda ya ce Najeriya ta samu daidaitaccen ci gaban tattalin arziki tsakanin 1999 da 2003.

“Lokacin da Obasanjo ya hau mulki a 1999, Najeriya ta samu ci gaban kashi 5.5 a 2000, amma zuwa 2003 kasar na samun kashi 9.5,” in ji shi, yana mai dagewa cewa duk da kura-kuranta, PDP ta fi APC aiki a fannoni da dama.

Hashim ya kuma soki abin da ya kira gazawar APC a bangaren wutar lantarki, yana zargin cewa gwamnatin ba ta kara ko megawatt guda ba cikin shekaru 10 da suka gabata.

“APC ba ta kara ko megawatt daya na wutar lantarki ba cikin shekaru 10,” in ji shi. Ya kuma yi zargin cewa maimakon fadada tattalin arziki, gwamnatin ta jagoranci koma baya.

“APC ba ta kara dala daya a GDP na Najeriya ba; maimakon haka ta lalata kusan kashi 50 na tattalin arzikinmu cikin shekaru 10,” ya kara da cewa.

A bangaren noma kuwa, Hashim ya ce Najeriya ta yi asarar kusan dala biliyan 4 na jarin samarwa cikin shekaru biyu a karkashin Shugaba Bola Tinubu, yana danganta hakan da yunkurin da ya kira na “tilasta saukar farashin abinci,” wanda ya ce ya raunana manoma tare da dagula tsarin samar da kayayyaki.

Ya ce tattalin arzikin kasar na bukatar ci gaba mai lamba biyu (double-digit growth) domin ya farfado, ba karamin ci gaba da ya kira na “maras tasiri” daga gyare-gyaren da suka gaza ba.

“Babban rage darajar Naira ya fara tun 1986; babu wani sabon abu ko kirkira a ciki,” in ji shi. Hashim ya kara da cewa tattalin arzikin Najeriya na bukatar wani shiri irin na John Maynard Keynes ko kuma irin tsare-tsaren jarumtaka na Roosevelt domin farfado da tattalin arzikin da ya shiga mawuyacin hali.

Da yake tsokaci kan kisan gillar da aka yi a al’ummar Woro da ke karamar hukumar Kaiama ta jihar Kwara, inda aka rawaito cewa kusan mutane 200 suka mutu, Hashim ya bayyana lamarin a matsayin babbar gazawar tsaro ta kasa.

Ya tambayi dalilin da ya sa jami’an tsaro suka kasa kai dauki duk da kusancin sansanin Sojojin Sama.

“Duk da cewa akwai sansanin Sojojin Sama da ke tazarar mintuna 15 kacal, an bar ‘yan ta’adda suka shiga suka kashe kusan mutane 200 ba tare da wata turjiya daga gwamnati ba,” in ji shi.

Hashim ya ce lamarin ya wuce gazawar tsaro kawai, yana mai cewa hakan na tayar da tambayoyi masu tayar da hankali kan yiwuwar akwai masu hannu a ciki.

GDP
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
Nenadi Usman Ta Fara Aiki A Ofishin jam’iyyar LP Amatsayin Shugaba

Nenadi Usman Ta Fara Aiki A Ofishin jam’iyyar LP Amatsayin Shugaba

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.