ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

GGI Da Kasar Sin Ta Gabatar Ta Samar Da Mafita Ga Kasashen Da Ke Cikin Mawuyacin Hali

by Sulaiman
8 months ago

“Babu mutane da yawa a can. An ce wurin mallakar Denmark ne, amma Denmark ba ta zuba masa ko sisi ba, kuma ba ta samar masa kariyar soja ba. An ce, a shekaru 300 da suka wuce, mutanen Denmark sun je wurin da jiragen ruwa, sai dai ina ganin a lokacin mu ma mun shiga jirgi mun je wurin.” Da muka zo karshen shekarar 2025, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya sake fara daukar mataki a kan tsibirin Greenland da ya nuna sha’awarsa tun farkon bana, inda ya nada gwamnan jihar Louisiana, Jeff Landry, a matsayin manzon kasar Amurka game da harkokin Greenland, kafin daga bisani ya yi kalaman na sama da ke ban dariya, kasancewar kowa ya san zuwa badi ne Amurka za ta cika shekaru 250 da kafuwa. Duk da haka, a wajen mai nuna fin karfi, ko tarihi ma ake iya sake rubutawa.

Alal hakika, matsalar Greenland ta shaida mawuyacin halin da kasa da kasa ke ciki ta fannin tsarin kulawa da harkokin duniya. In mun waiwayi shekarar 2025 da ke dab da karewa, za mu tarar da cewa: Rasha da Ukraine na ci gaba da gwabza fada da juna, wanda da wuya a ga karshensa, kuma rikicin da ya auku tsakanin Palasdinu da Isra’ila ya haifar da hasarorin rayuka sama da dubu 70, tare da raba mutane kusa miliyan biyu da muhallansu, duk da haka, Amurka ta yi ta jefa kuri’ar kin amincewa da daftarin tsagaita bude wuta da kwamitin sulhun MDD ya gabatar, har wa yau, shugaba Trump ya dauki matakin haraji na yi-min-na-rama kan kasashen duniya, wanda ya yi matukar lalata tsarin ciniki na tsakanin bangarori da dama… Lallai ana kara fuskantar matsalolin da suka shafi tsarin da muke da su wajen kulawa da harkokin duniya.

Sai dai abin farin ciki shi ne, a fuskantar matsalolin da ke gabansu, kasashe masu tasowa na kara hada kawunansu tare da daukar kwararan matakai, har ma suka zamanto wani muhimmin rukuni na inganta tsarin kulawa da harkokin duniya.

ADVERTISEMENT

A wannan shekara, duniya ta shaida muhimmiyar rawar da kasar Sin ke takawa wajen inganta tsarin kulawa da harkokin duniya. Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar inganta tsarin kulawa da harkokin duniya, wato GGI a takaice, wanda hakan ya samar da gudummawar kasar wajen kara tabbatar da adalci ga tsarin kulawa da harkokin duniya, tare da karfafa matsayin MDD wajen jagorantar harkokin duniya. Kamar yadda Bahaushe kan ce, “faduwa ta zo daidai da zama”, shawarar ta samu goyon baya daga kasashe da kungiyoyin duniya sama da 150. Darektan cibiyar nazarin harkokin kasar Sin ta Nijeriya, Charles Onunaiju ya ce, shawarar GGI ta kara wakilcin kasashe masu tasowa tare da kara fitowa da muryarsu, wanda hakan abu ne da Nijeriya da sauran kasashen Afirka suka dade suna nema.

A wannan shekara kuma, kasashen Brazil da Afirka ta Kudu sun karbi bakuncin shirya taron kolin BRICS da na G20, kasar Brazil a nata bangaren ta kuma shirya taron MDD kan sauyin yanayi. Abin lura shi ne, kasashe mahalarta taron MDD kan sauyin yanayi sun cimma daidaito ba tare da halartar kasar Amurka ba, matakin da masanan kasa da kasa suke kallonsa a matsayin sanarwar kasashe masu tasowa na dukufa a kan kafa tsarin kulawa da harkokin duniya mai karin adalci.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

A wannan shekara, kasashen Afirka sun ci gaba da kokarin kare adalcinsu, inda suka ci gaba da korar sojojin kasashen yamma, har Faransa ta mika wasu sansanonin soja biyu ga Senegal, matakin da ya kawo karshen girke sojojin da kasar ta yi a kasashen yammacin Afirka da na tsakiyar nahiyar. Har wa yau, kungiyar tarayyar Afirka ta kira taron koli da ke da taken “kiyaye adalci ga ’yan Afirka da zuriyoyinsu ta hanyar biyan diyya”, wanda ya isar da sakon kasashen Afirka na tsayawa a kan kafafuwansu da ma gyara kura-kuran da aka tafka musu a tarihi. Sai kuma a Nijeriya, gwamnatin kasar ta ki yarda da bukatar kasar Amurka game da karbar bakin haure da ta kora daga kasar, duk da matsin lamba da kasar ta yi mata.

Idan muka waiwayi shekarar 2025, za mu ga cewa, ta kasance mai muhimmanci wajen gyare-gyaren tsarin kulawa da harkokin duniya. A yayin da ake fuskantar karin nuna fin karfi da rarabuwar kawuna a tsakanin kasashen duniya, kasar Sin na hada hannu da kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa bisa shawarar GGI, don kafa tsarin kulawa da harkokin duniya mai adalci. A zahiri ne, shawarar na bude wani sabon babi game da makomar dan Adam.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Saƙon Sakatare Janar Na MDD, Antonio Guterres Na Shiga Sabuwar Skekarar 2026

Saƙon Sakatare Janar Na MDD, Antonio Guterres Na Shiga Sabuwar Skekarar 2026

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.