Kasar Ghana ta gabatar da shawarar zurfafa hadin gwiwa tsakaninta da Sin da sauran kasashen yammacin Afrika, domin inganta bangaren kiwon lafiya na yankin.
Mataimakiyar ministan lafiya na Ghana Grace Ayensu-Danquah ce ta bukaci hakan yayin taron baje kolin kayayyakin kiwon lafiya da binciken lafiya ta amfani da fasahar AI karo na 3, inda ta ce ya kamata hadin gwiwa da Sin a bangaren lafiya ya zarce sayen kayayyaki, zuwa sarrafawa da harhadawa a cikin gida da musayar fasaha da hadin gwiwa a bangaren bincike da horon kwararru da zuba jari wajen bunkasa kwarewa a cikin gida.
Ta ce da wannan, kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS) za ta samu karin karfi a bangaren kiwon lafiya da kirkiro ayyukan yi, tare da bayar da gudumuwa wajen samun tsarin kiwon lafiya mai karin juriya.
Ta ce hadin gwiwar Ghana da Sin na samar da muhimman damarmakin cin gajiyar kwarewar Sin a bangaren kera kayayyaki da aikin injiniya da fasaha da kayayyakin kiwon lafiya, domin taimaka wa burikan da Ghana ke da su a bangaren kiwon lafiya. (Fa’iza Mustapha)














