Ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar ya nuna damuwa kan ƙaruwar ayyukan ta’addanci a Jihar Sakkwato tare da cewar wajibi ne gwamnati ta kawo ƙarshen kisan kiyashin da ake yi wa jama’a.
Atiku, tsohon mataimakin shugaban ƙasa, ya bayyana cewa abin takaici ne kisan gillar da ɓarayin daji suka yi wa mutane 32 a Sakkwato ba tare da sun aikata ko wane irin laifi ba.
A jawabin da ya fitar, Atiku ya ce kashe- kashen sun zama tamkar ruwan dare, lamarin da ke ban tsaro wanda bai kamata gwamnatin da ta kasa kare ƴan ƙasarta ba, babu alfanu fitar da sanarwar jaje bayan kowanne kisan gilla ba tare da ɗaukar ƙwaƙƙwaran matakin shawo kan matsalar ba.
A makon jiya ne ɗaruruwan ɓarayin daji suka shiga garin Ungushi da ke ƙaramar hukumar Keɓɓe da ke Kudancin Sakkwato, suka ɗauki rayukan mutanen a yayin da suke Sallar Juma’a.
Majiyoyi da dama sun bayyana cewar ɓarayin dajin sun fara kai hari ne a cikin garin Keɓɓe, inda suka fatattaki jami’an tsaro da al’ummar garin tare da fashe shaguna da awon gaba da dabbobi, daga bisani kuma suka kutsa kai a cikin ƙauyuka.
Wani shugaba a yankin wanda ya halarci jana’izar da aka gudanar ranar Lahadi, ya ce mazauna yankin sun gano tare da bizne gawarwakin mutane 32, ya kuma bayyana cewa mazauna yankin sun kashe mutane 13 daga cikin maharan a yayin artabun da aka shafe tsawon lokaci.
Atiku ya jaddada cewar babban aikin gwamnati shi ne, kare rayukan al’umma, don haka ƴan Nijeriya ba za su ci gaba da bizne ƴan‘uwansu ba, yayin da waɗanda aka ɗora wa alhakin tsaron suke ta bayar da uzuri.
“Zuciyata na tare da iyalan waɗanda suka rasa rayukansu da kuma al’ummar Jihar Sakkwato, amma ta’aziyya kaɗai ba ta isa ba. Mutane nawa ne kuma za a kashe kafin gwamnati ta ɗauki kare rayukan ƴan ƙasa a matsayin abin gaggawa?” cewar Atiku.














