ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Guguwar Kudin Fito Na Gwamnatin Trump: Dabara Ko Hauka?

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
{"data":{"imageEffectId":"","activityName":"","effect_id":"erase","appversion":"12.0.0","capability_key":["erase"],"effect_type":"tool","product":"retouch","playId":"","os":"ios","pictureId":"79E8B7D8-A99F-484F-88F1-8D4843281E28","capability_extra_v2":{"erase":[{"panel":"eliminatePen"}]},"stickerId":"","enter_from":"enter_launch","infoStickerId":"","filterId":""},"source_type":"douyin_beauty_me"}

{"data":{"imageEffectId":"","activityName":"","effect_id":"erase","appversion":"12.0.0","capability_key":["erase"],"effect_type":"tool","product":"retouch","playId":"","os":"ios","pictureId":"79E8B7D8-A99F-484F-88F1-8D4843281E28","capability_extra_v2":{"erase":[{"panel":"eliminatePen"}]},"stickerId":"","enter_from":"enter_launch","infoStickerId":"","filterId":""},"source_type":"douyin_beauty_me"}

“Hauka,” “wauta” da “rashin hankali” su ne kalmomin da masharhanta ke amfani da su wajen bayyana ra’ayoyinsu game da matakin kakaba harajin fito da shugaban Amurka Donald Trump ya dauka a ranar da ya yiwa lakabi da “Ranar ‘Yanci,” wato ranar 2 ga Afrilu. Babu abin da ya fi faranta ran Trump sama da ya wayi gari ya ga kansa tsaye a lambunsa na Rose Garden rike da takarda mai dauke da jerin sunayen kasashen da zai kakaba wa sabon haraji a karkashin manufarsa ta “Make American Great Again” wato MAGA a takaice. Bayan sanin kowa ne cewa da yawa daga cikin kasashen da ya kakaba wa sabon harajin fiton kananan kasashe ne da ke rayuwa cikin kangin talauci, don me kasashe kamar su Lesotho, Laos, da Kambodiya za su biya karin kudin fito don kawai Amurka ta wadata? Shin sun ba da gudummawa ga rasa yawancin masana’antun da Amurka ta yi cikin tsawon shekaru ta hanyar manufofin mika masana’antunta da kuma karfinta na kwadago ga kasashe masu arhan kwadago ne? Shin wadannan al’ummomi ne ke da alhakin durkushewar biranen Amurka har suka zama tamkar yankin marasa galihu, da yankunan masana’antu na Amurka da suka zama kamar kufai? Mene ne laifin gungun bakarariyar tsibiri, da dutse mai aman wuta da ke kusa da Antarctica, wanda ke lullube da dusar kankara dake zama gida ga dabbobin Penguin da ya laftawa harajin fito kashi 10 cikin dari, me za mu kira wannan in ba hauka ba?

 

Manufar harajin Trump ba wani abu ba ne illa yunkurin sanya kasashen duniya samar da kudaden da zai yi amfani da su wajen farfado da tattalin arzikin Amurka. Daular Birtaniya ta aiwatar da irin wannan manufar a karni na 19 lokacin da ta azurta ’yan jarin hujja na Birtaniya yayin da ta tatse dukiyar Afirka da Asiya ta hanyar mulkin mallaka. Ganin cewa barazanar ta riga ta tayar da kura a kasuwannin duniya, lamarin da ya tilastawa Trump kira da a dakatar da matakin na tsawon kwanaki 90 kafin aiwatar da shi, wato a kan dukkan sauran kasashe amma ban da kasar Sin, wanda daga bisani ya laftawa karin harajin fito kashi 145 cikin dari. Masharhanta na ganin togaice kasar Sin da Trump ya yi wani yunkuri ne rage rawar da kasar Sin ke takawa a duniya musamman a hadin gwiwarta da kasashe masu tasowa karkashin shawarar “Ziri daya da Hanya daya”, saboda a ganinsa gurgunta tattalin arziki Sin zai kawo koma baya ga kasashe masu tasowa ta yadda za su dawo su rusuna gaban Amurka don neman mafita. Da yawa daga cikin wadannan kasashe masu tasowa sun san wannan gaskiyar. Yayin da za su dan numfasa tsawon kwanaki 90 kafin tsarin harajin fiton ya sake rike musu wuya, sun san wanene abokinsu kuma wanene makiyinsu.

ADVERTISEMENT

 

Idan akwai wata hanyar magance wannan haukar, to tana iya zama mai ban mamaki, saboda a tarihin Amurka na manufofin neman sassaucin ra’ayi tun daga shekarar 1980, tsarin biyan haraji na Amurka ya zama mafi cutarwa, wanda ke dora kason haraji mafi girma kan Amurkawa talakawa da kananan ma’aikata tare da dora mafi kankantar haraji kan masu arziki. (Mohammed Yahaya)

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

 

Trump
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Trump
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Sin Na Maraba Da Masu Zuba Jari Domin Su More Damammakin Bunkasarta

Sin Na Maraba Da Masu Zuba Jari Domin Su More Damammakin Bunkasarta

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.