ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Manyan Ayyuka A Anka Ta Zamfara

by Sulaiman
5 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sake jaddada ƙudirin sa na tabbatar da cewa jihar Zamfara ta shiga sahun jihohin da ke kan turbar ci gaba mai ɗorewa da amfanar al’umma baki ɗaya.

 

A ranar Talata ne gwamnan ya ƙaddamar da manyan ayyukan raya ƙasa guda huɗu a Ƙaramar Hukumar Anka, a wani mataki da ke nuna cikar alƙawuran da ya ɗauka ga al’ummar yankin.

ADVERTISEMENT
  • Saka Ya Rattaba Hannu Akan Karin Kwantiragin Shekaru 5 A Arsenal 
  • Dokar Zaɓe: An Harba Barkonon Tsohuwa Ga Masu Zanga-zanga A Majalisa

A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ayyukan da aka ƙaddamar sun haɗa da sake gina da kuma cikakken gyaran fadar Sarkin Zamfaran Anka tare da saka kayan zamani, fara aikin titin Anka–Abbare, da kuma gina sabuwar sakatariyar Ƙaramar Hukumar Anka.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Sauran ayyukan da aka fara sun haɗa da gina ofisoshin Hukumar Hisbah da Rundunar Kare Al’umma (CPG), tare da sake gina makarantar SAFE School da ke Anka domin samar da yanayi mai tsaro da inganci ga ɗalibai.

 

A jawabin da ya gabatar, Gwamna Lawal ya bayyana cewa ziyarar tasa zuwa Anka na daga cikin cika alƙawuran yaƙin neman zabensa ga al’ummar Anka da ma jihar Zamfara baki ɗaya.

 

Ya ce ƙaddamar da sabuwar fadar Sarkin Anka da Majalisar Sarakunan Zamfara na daga cikin muhimman matakan da ke mayar da martaba da kimar masarautun gargajiya, waɗanda su ne ginshiƙan al’ada da tarihi.

 

Gwamnan ya kuma jaddada cewa fara aikin titin Anka–Abbare zai inganta hanyoyin zirga-zirga zuwa yankunan karkara, ya bunƙasa kasuwanci, tare da samar da tasirin tattalin arziki mai yawa ga al’umma.

 

Ya ƙara da cewa, ɗaya daga cikin muhimman hanyoyin ceto Zamfara shi ne dawo da kima, daraja da nagartar aikin gwamnati ta hanyar samar da ingantaccen wurin aiki ga ma’aikata a matakin jiha da na ƙananan hukumomi. Saboda haka ne aka fara gina sabon sakatariyar ƙaramar hukuma a Anka.

 

Gwamnan ya bayyana cewa babu wata al’umma da za ta ɗore ba tare da bin doka da oda ba, don haka samar da ofisoshi ga Hisbah da CPG zai taimaka musu wajen gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

 

Dangane da ilimi, Gwamna Lawal ya ce ilimi shi ne ginshiƙin kowace al’umma mai tasowa, don haka sake gina SAFE School a Anka wani bangare ne na shirin gaggawa na samar da muhalli mai tsaro da dacewa ga ɗalibai.

 

Ya ƙara da cewa, bayan maddamar da ayyuka a masarautar Anka da Tsafe, nan ba da jimawa ba za a ƙaddamar da ayyuka a Kaura Namoda da Moriki. Haka kuma ayyuka a Bungudu, Bukkuyum da Zurmi na gudana kuma za a kammala su tare da ƙaddamar da su kafin ƙarshen shekarar nan, In Sha Allah.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Zaben Neja: APC Ta Yi Nasara A Kananan Hukumomi 22 Daga Cikin 25 

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A Jam'iyyar APC A Kano

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.