ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Manyan Ayyuka A Anka Ta Zamfara

by Sulaiman
7 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sake jaddada ƙudirin sa na tabbatar da cewa jihar Zamfara ta shiga sahun jihohin da ke kan turbar ci gaba mai ɗorewa da amfanar al’umma baki ɗaya.

 

A ranar Talata ne gwamnan ya ƙaddamar da manyan ayyukan raya ƙasa guda huɗu a Ƙaramar Hukumar Anka, a wani mataki da ke nuna cikar alƙawuran da ya ɗauka ga al’ummar yankin.

ADVERTISEMENT
  • Saka Ya Rattaba Hannu Akan Karin Kwantiragin Shekaru 5 A Arsenal 
  • Dokar Zaɓe: An Harba Barkonon Tsohuwa Ga Masu Zanga-zanga A Majalisa

A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ayyukan da aka ƙaddamar sun haɗa da sake gina da kuma cikakken gyaran fadar Sarkin Zamfaran Anka tare da saka kayan zamani, fara aikin titin Anka–Abbare, da kuma gina sabuwar sakatariyar Ƙaramar Hukumar Anka.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Sauran ayyukan da aka fara sun haɗa da gina ofisoshin Hukumar Hisbah da Rundunar Kare Al’umma (CPG), tare da sake gina makarantar SAFE School da ke Anka domin samar da yanayi mai tsaro da inganci ga ɗalibai.

 

A jawabin da ya gabatar, Gwamna Lawal ya bayyana cewa ziyarar tasa zuwa Anka na daga cikin cika alƙawuran yaƙin neman zabensa ga al’ummar Anka da ma jihar Zamfara baki ɗaya.

 

Ya ce ƙaddamar da sabuwar fadar Sarkin Anka da Majalisar Sarakunan Zamfara na daga cikin muhimman matakan da ke mayar da martaba da kimar masarautun gargajiya, waɗanda su ne ginshiƙan al’ada da tarihi.

 

Gwamnan ya kuma jaddada cewa fara aikin titin Anka–Abbare zai inganta hanyoyin zirga-zirga zuwa yankunan karkara, ya bunƙasa kasuwanci, tare da samar da tasirin tattalin arziki mai yawa ga al’umma.

 

Ya ƙara da cewa, ɗaya daga cikin muhimman hanyoyin ceto Zamfara shi ne dawo da kima, daraja da nagartar aikin gwamnati ta hanyar samar da ingantaccen wurin aiki ga ma’aikata a matakin jiha da na ƙananan hukumomi. Saboda haka ne aka fara gina sabon sakatariyar ƙaramar hukuma a Anka.

 

Gwamnan ya bayyana cewa babu wata al’umma da za ta ɗore ba tare da bin doka da oda ba, don haka samar da ofisoshi ga Hisbah da CPG zai taimaka musu wajen gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

 

Dangane da ilimi, Gwamna Lawal ya ce ilimi shi ne ginshiƙin kowace al’umma mai tasowa, don haka sake gina SAFE School a Anka wani bangare ne na shirin gaggawa na samar da muhalli mai tsaro da dacewa ga ɗalibai.

 

Ya ƙara da cewa, bayan maddamar da ayyuka a masarautar Anka da Tsafe, nan ba da jimawa ba za a ƙaddamar da ayyuka a Kaura Namoda da Moriki. Haka kuma ayyuka a Bungudu, Bukkuyum da Zurmi na gudana kuma za a kammala su tare da ƙaddamar da su kafin ƙarshen shekarar nan, In Sha Allah.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Zaben Neja: APC Ta Yi Nasara A Kananan Hukumomi 22 Daga Cikin 25 

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A Jam'iyyar APC A Kano

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.