Sabon rikici ya ɓarke a jam’iyyar APC a Jihar Kano bayan wani taron haɗin kai da aka gudanar a ranar Talata a jihar.
Taron ya haɗa da shugaban APC na ƙasa Nentawe Yilwatda, gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, da sauran manyan jiga-jigan jam’iyyar domin tattauna yadda za a ƙarfafa haɗin kai.
- SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1
- Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Taraktoci 2,000 Domin Noman Hekta Miliyan 1.5
A wajen taron, shugaban jam’iyyar ya ce za a yi amfani da tsarin rabon shugabanci na kashi 60 da kashi 40 tsakanin sabbin mambobi da tsofaffin ‘yan jam’iyyar.
Sai dai bayan taron, wani bidiyo ya karaɗe kafafen sada zumunta, inda aka ga ɗan majalisa Alhassan Ado Doguwa cikin fushi yana cewa Sanata Kawu Sumaila da Abdullahi Tijjaniya Muhammad Gwarzo ba za su sauya siyasar Doguwa da Tudun Wada yadda suke so ba.
Haka kuma wani bidiyo ya nuna Sanata Kawu yana bai wa Doguwa shawara bayan taron miƙa tutar jam’iyyar, lamarin da ake ganin rikicin na iya raba kan mambobinta.
Masu sharhi a kan siyasa sun yi gargaɗin cewa siyasar Kano na iya shiga mawuyacin hali idan shugabannin APC ba su haɗa kai ba.















Discussion about this post