ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Amince Da Wani Shirin Gaggawa Don Ceto Ilimi A Zamfara

by Sulaiman
2 months ago

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da wani shiri na musamman na kwanaki 120 domin magance manyan matsalolin da ke addabar tsarin ilimi a jihar.

Gwamnan ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar 65 a Gidan Gwamnati da ke Gusau a ranar Litinin, inda aka tattauna muhimman batutuwa da suka shafi bangarori daban-daban, ciki har da ilimi, lafiya da ayyukan raya ƙasa.

A cewar wata sanarwa, “A zaman Majalisar zartarwar na 65, gwamnatin ta amince da wani tsari na gaggawa da aka gina ne bisa bincike da nazarin da Ma’aikatar Ilimi da Hukumar Tabbatar da Ingancin Ilimi ta Jihar (EQAA) suka gudanar a baya.”“Shirin na kwanaki 120, wanda muƙaddashin Kwamishinan Ilimi, Abdulmalik Abubakar Gajam ya gabatar, ya ƙunshi matakai da suka haɗa da tantance ma’aikata ta hanyar duba albashi, tsara taswirar makarantu da kuma duba yanayin gine-ginen makarantu.

ADVERTISEMENT

Haka kuma, shirin ya tanadi aiwatar da sauye-sauye cikin gaggawa a bangarorin gudanarwa, gine-gine, fasahar zamani, horas da malamai da kuma kula da jin daɗin ɗalibai, domin tabbatar da ingantaccen tsarin ilimi a jihar.

Bugu da ƙari, Majalisar ta amince da kafa wani kwamiti na haɗin gwiwa ƙarƙashin jagorancin Ma’aikatar Ilimi, Kimiyya da Fasaha, domin bincike da tantance dukkan gine-ginen da aka gina ba bisa ƙa’ida ba a kusa da makarantu.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

An kuma ba kwamitin umarnin ɗaukar matakin kwashe irin waɗannan gine-gine domin tabbatar da tsaro da tsaftar muhallin makarantu.

A wani muhimmin mataki, Majalisar ta amince da samar da dokar haɗaka guda ɗaya da za ta rufe dukkan matakan ilimi daga na yara ƙanana (ECCDE) zuwa manyan makarantu. An bayyana cewa za a gabatar da ƙudirin dokar ga Majalisar Dokokin Jihar domin amincewa da shi cikin gaggawa.

Haka kuma, Gwamna Lawal ya amince da sauya tsarin biyan albashi ga ma’aikatan da ba malamai ba, inda za a mayar da su zuwa wasu ma’aikatun gwamnati ko kuma kamfanoni masu zaman kansu, domin inganta tsarin aiki da rage cunkoso a bangaren ilimi.

Majalisar ta kuma amince da kafa Kwamitin Jagoranci na Jihar kan Dokar Ta-baci a Fannin Ilimi, tare da bai wa kwamitin damar kafa Kwamitin Kwararru (Technical Working Group) da kuma haɗa gwiwa da masu ruwa da tsaki kamar Ƙungiyar Malamai (NUT), UNICEF, Hukumar Ilimin Firamare ta Tarayya (UBEC), shugabannin gargajiya da na addini, masu makarantu masu zaman kansu da ƙungiyoyin farar hula.

Wannan mataki na nuna ƙudirin gwamnatin Zamfara na farfaɗo da bangaren ilimi, tare da tabbatar da cewa an magance matsalolin da suka daɗe suna tarnaƙi ga cigaban ilimi a jihar.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Firaministan Kasar Sifaniya

Xi Jinping Ya Gana Da Firaministan Kasar Sifaniya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.