ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Amince Da Wani Shirin Gaggawa Don Ceto Ilimi A Zamfara

by Sulaiman
3 months ago

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da wani shiri na musamman na kwanaki 120 domin magance manyan matsalolin da ke addabar tsarin ilimi a jihar.

Gwamnan ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar 65 a Gidan Gwamnati da ke Gusau a ranar Litinin, inda aka tattauna muhimman batutuwa da suka shafi bangarori daban-daban, ciki har da ilimi, lafiya da ayyukan raya ƙasa.

A cewar wata sanarwa, “A zaman Majalisar zartarwar na 65, gwamnatin ta amince da wani tsari na gaggawa da aka gina ne bisa bincike da nazarin da Ma’aikatar Ilimi da Hukumar Tabbatar da Ingancin Ilimi ta Jihar (EQAA) suka gudanar a baya.”“Shirin na kwanaki 120, wanda muƙaddashin Kwamishinan Ilimi, Abdulmalik Abubakar Gajam ya gabatar, ya ƙunshi matakai da suka haɗa da tantance ma’aikata ta hanyar duba albashi, tsara taswirar makarantu da kuma duba yanayin gine-ginen makarantu.

ADVERTISEMENT

Haka kuma, shirin ya tanadi aiwatar da sauye-sauye cikin gaggawa a bangarorin gudanarwa, gine-gine, fasahar zamani, horas da malamai da kuma kula da jin daɗin ɗalibai, domin tabbatar da ingantaccen tsarin ilimi a jihar.

Bugu da ƙari, Majalisar ta amince da kafa wani kwamiti na haɗin gwiwa ƙarƙashin jagorancin Ma’aikatar Ilimi, Kimiyya da Fasaha, domin bincike da tantance dukkan gine-ginen da aka gina ba bisa ƙa’ida ba a kusa da makarantu.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

An kuma ba kwamitin umarnin ɗaukar matakin kwashe irin waɗannan gine-gine domin tabbatar da tsaro da tsaftar muhallin makarantu.

A wani muhimmin mataki, Majalisar ta amince da samar da dokar haɗaka guda ɗaya da za ta rufe dukkan matakan ilimi daga na yara ƙanana (ECCDE) zuwa manyan makarantu. An bayyana cewa za a gabatar da ƙudirin dokar ga Majalisar Dokokin Jihar domin amincewa da shi cikin gaggawa.

Haka kuma, Gwamna Lawal ya amince da sauya tsarin biyan albashi ga ma’aikatan da ba malamai ba, inda za a mayar da su zuwa wasu ma’aikatun gwamnati ko kuma kamfanoni masu zaman kansu, domin inganta tsarin aiki da rage cunkoso a bangaren ilimi.

Majalisar ta kuma amince da kafa Kwamitin Jagoranci na Jihar kan Dokar Ta-baci a Fannin Ilimi, tare da bai wa kwamitin damar kafa Kwamitin Kwararru (Technical Working Group) da kuma haɗa gwiwa da masu ruwa da tsaki kamar Ƙungiyar Malamai (NUT), UNICEF, Hukumar Ilimin Firamare ta Tarayya (UBEC), shugabannin gargajiya da na addini, masu makarantu masu zaman kansu da ƙungiyoyin farar hula.

Wannan mataki na nuna ƙudirin gwamnatin Zamfara na farfaɗo da bangaren ilimi, tare da tabbatar da cewa an magance matsalolin da suka daɗe suna tarnaƙi ga cigaban ilimi a jihar.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Firaministan Kasar Sifaniya

Xi Jinping Ya Gana Da Firaministan Kasar Sifaniya

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.