Da safiyar yau Talata 14 ga watan nan, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da firaministan kasar Sifaniya Pedro Sanchez, wanda a yanzu haka ke ziyarar aiki a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.
A yayin ganawar, Xi ya ce, duk da tashin-tashina da sauye-sauyen da ake ciki a duniya, dangantakar Sin da Sifaniya na bunkasa yadda ya kamata, dangantakar da aka raya bisa manyan tsare-tsare, kuma daya daga cikin dalilan samun nasara shi ne, yanke shawara bisa muradun bai daya.Shugaba Xi ya jaddada cewa, tsayawa kan gaskiya da nuna fin karfi na kalubalantar juna yanzu haka a duniya.
Yadda za a fuskanci dokokin kasa da kasa da zaman odar duniya, na nuna akidun wata kasa baro-baro a fili. Sin da Sifaniya, kasashe ne masu girmama ka’idoji da rikon amana, ya dace su kara tuntubar juna, da inganta samun fahimtar juna, da habaka hadin gwiwa, tare kuma da kin yarda da mayar da duniya ta koma baya zuwa bin manufar nuna fin karfi.
A nasa bangaren kuwa, firaministan Sifaniya, Pedro Sanchez ya ce, ya kawo ziyarar aiki kasar Sin har sau hudu a cikin shekaru hudu, al’amarin da ya nuna cewa, dukkan kasashen biyu suna maida hankali sosai kan alakokinsu.
Yayin da duniya ke fama da yanayi mai sarkakiya da tashe-tashen hankula da dama, muddin aka tsaya ga ra’ayin kara cudanya tsakanin mabambantan bangarori, da gina duniya mai mabambantan sassa, duniyarmu za ta samu zaman lafiya mai dorewa.
Kasar Sifaniya tana adawa da “sabon yakin cacar baka”, da “katse huldar tattalin arziki da kasar Sin”, akasin haka, tana goyon-bayan kasashen Turai su kara tuntuba da kasar Sin tare da fadada hadin gwiwa. (Murtala Zhang)















Discussion about this post