ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Yi Farin Ciki Da Gwajin Jirgi Na Farko A Filin Jirgin Sama Na Ƙasa Da Ƙasa Na Gusau

by Sulaiman
3 months ago
Gusau

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana matuƙar farin cikinsa bayan nasarar gudanar da gwajin saukar jirgi na farko a sabon Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa da ke Gusau.

 

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an bayyana cewa jirgin gwajin ya sauka da misalin ƙarfe 4:30 na yammacin ranar Lahadi, a wani lamari da aka bayyana a matsayin tarihi ga jihar.

ADVERTISEMENT
  • 2027: Cikin Ƴan APC Ya Ɗuri Ruwa Saboda Tasirin Makinde  – Ƙungiyar PDP
  • Kano Pillars Ta Doke Enyimba, Ta Matsa Gaba A Teburin Gasar NPFL

Sanarwar ta ƙara da cewa jirgin da aka yi amfani da shi, nau’in Bombardier Challenger 605, mallakin Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ne, wanda aka tura domin tantance inganci da shirye-shiryen filin jirgin kafin fara amfani da shi a hukumance.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gwande A Jihar Filato

Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

A cewar sanarwar, wannan rana za ta kasance abin tunawa a tarihin Zamfara, kasancewar gwamnan ya shaida saukar jirgi na farko a filin jirgin da aka daɗe ana jira.

 

An bayyana cewa jirgin mai lambar rajista 5N-FGZ ya gudanar da gwaji na musamman domin tantance yadda filin jirgin zai iya karɓar manyan baƙi (VIP), musamman gabanin wasu muhimman zirga-zirga da ake sa ran yi a mako mai zuwa.

 

An kuma gudanar da wannan gwaji ne bisa tanade-tanaden dokokin sufurin jiragen sama na Nijeriya (Nigeria Civil Aviation Regulations), inda aka bi duk ƙa’idojin tsaro da aiki.

 

Kafin gudanar da gwajin, gwamnatin jihar ta nemi izini daga Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Nijeriya (NCAA), wadda ta bayar da amincewa ta musamman wato No Technical Objection (NTO) domin saukar jirgin a Gusau.

 

Haka kuma, an gudanar da aikin jirgin ne bisa tsarin Visual Flight Rules (VFR), wanda ke nufin an yi zirga-zirgar ne a tsakanin fitowar rana zuwa faɗuwarta, kamar yadda ƙa’ida ta tanada.

 

Wannan gagarumin ci gaba ya ƙara ɗaga darajar gwamnatin Gwamna Lawal, musamman idan aka yi la’akari da cewa tun bayan kafuwar Jihar Zamfara sama da shekaru 30 da suka gabata, ba ta taɓa samun filin jirgin sama irin wannan ba.

Gusau
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar
  • Sulaiman
    Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU
  • Sulaiman
    Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku
  • Sulaiman
    Kasar Sin Za Ta Habaka Bude Fannonin Hada-Hadar Kudi Ga Duniya

MASU ALAKA

’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya, Sun Sace Limami Da Wasu Mutane 7 A Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gwande A Jihar Filato

June 18, 2026
Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

June 18, 2026
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Manoma 7 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Sakkwato, Sun Ƙwato Babura

June 17, 2026
Next Post
PDP

Daƙile Taron Ƙasa Na Abuja: Ɓangaren PDP Ƙarƙashin Turaki Ya Caccaki Ɓangaren Wike 

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya, Sun Sace Limami Da Wasu Mutane 7 A Filato

‘Yan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gwande A Jihar Filato

June 18, 2026
Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

June 18, 2026
Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

June 17, 2026
Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

June 17, 2026
Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

June 17, 2026
Kasar Sin Za Ta Habaka Bude Fannonin Hada-Hadar Kudi Ga Duniya

Kasar Sin Za Ta Habaka Bude Fannonin Hada-Hadar Kudi Ga Duniya

June 17, 2026
Sin Na Gaggauta Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Kasa Da Kasa

Sin Na Gaggauta Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Kasa Da Kasa

June 17, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Takardar Bayani Game Da Inganta Tsarin Jagorancin Harkokin Duniya

Kasar Sin Ta Gabatar Da Takardar Bayani Game Da Inganta Tsarin Jagorancin Harkokin Duniya

June 17, 2026
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Ceto Manoma 7 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Sakkwato, Sun Ƙwato Babura

June 17, 2026
Liu Guozhong Ya Halarci Taron Koli Kan Yadda Kasashen Afirka Za Su Fuskanci Cutar Ebola

Liu Guozhong Ya Halarci Taron Koli Kan Yadda Kasashen Afirka Za Su Fuskanci Cutar Ebola

June 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.