ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Yi Farin Ciki Da Gwajin Jirgi Na Farko A Filin Jirgin Sama Na Ƙasa Da Ƙasa Na Gusau

by Sulaiman
4 months ago
Gusau

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana matuƙar farin cikinsa bayan nasarar gudanar da gwajin saukar jirgi na farko a sabon Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa da ke Gusau.

 

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an bayyana cewa jirgin gwajin ya sauka da misalin ƙarfe 4:30 na yammacin ranar Lahadi, a wani lamari da aka bayyana a matsayin tarihi ga jihar.

ADVERTISEMENT
  • 2027: Cikin Ƴan APC Ya Ɗuri Ruwa Saboda Tasirin Makinde  – Ƙungiyar PDP
  • Kano Pillars Ta Doke Enyimba, Ta Matsa Gaba A Teburin Gasar NPFL

Sanarwar ta ƙara da cewa jirgin da aka yi amfani da shi, nau’in Bombardier Challenger 605, mallakin Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ne, wanda aka tura domin tantance inganci da shirye-shiryen filin jirgin kafin fara amfani da shi a hukumance.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

A cewar sanarwar, wannan rana za ta kasance abin tunawa a tarihin Zamfara, kasancewar gwamnan ya shaida saukar jirgi na farko a filin jirgin da aka daɗe ana jira.

 

An bayyana cewa jirgin mai lambar rajista 5N-FGZ ya gudanar da gwaji na musamman domin tantance yadda filin jirgin zai iya karɓar manyan baƙi (VIP), musamman gabanin wasu muhimman zirga-zirga da ake sa ran yi a mako mai zuwa.

 

An kuma gudanar da wannan gwaji ne bisa tanade-tanaden dokokin sufurin jiragen sama na Nijeriya (Nigeria Civil Aviation Regulations), inda aka bi duk ƙa’idojin tsaro da aiki.

 

Kafin gudanar da gwajin, gwamnatin jihar ta nemi izini daga Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Nijeriya (NCAA), wadda ta bayar da amincewa ta musamman wato No Technical Objection (NTO) domin saukar jirgin a Gusau.

 

Haka kuma, an gudanar da aikin jirgin ne bisa tsarin Visual Flight Rules (VFR), wanda ke nufin an yi zirga-zirgar ne a tsakanin fitowar rana zuwa faɗuwarta, kamar yadda ƙa’ida ta tanada.

 

Wannan gagarumin ci gaba ya ƙara ɗaga darajar gwamnatin Gwamna Lawal, musamman idan aka yi la’akari da cewa tun bayan kafuwar Jihar Zamfara sama da shekaru 30 da suka gabata, ba ta taɓa samun filin jirgin sama irin wannan ba.

Gusau
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal
  • Sulaiman
    Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba
  • Sulaiman
    An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
  • Sulaiman
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

MASU ALAKA

Gusau
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Gusau
Labarai

Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

July 25, 2026
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe
Rahotonni

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026
Next Post
PDP

Daƙile Taron Ƙasa Na Abuja: Ɓangaren PDP Ƙarƙashin Turaki Ya Caccaki Ɓangaren Wike 

LABARAI MASU NASABA

Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam

Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam

July 25, 2026
Wane Ne Khalil Al-Hayya, Sabon Shugaban Kungiyar Hamas?

Wane Ne Khalil Al-Hayya, Sabon Shugaban Kungiyar Hamas?

July 25, 2026
Tsakanin Digiri Da Sana’a Wanne Ya Fi Muhimmanci A Wannan Lokacin?

Tsakanin Digiri Da Sana’a Wanne Ya Fi Muhimmanci A Wannan Lokacin?

July 25, 2026
Gusau

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

July 25, 2026
Gusau

Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

July 25, 2026
Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

July 25, 2026
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026
Gusau

Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu

July 25, 2026
Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.