ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Yi Farin Ciki Da Gwajin Jirgi Na Farko A Filin Jirgin Sama Na Ƙasa Da Ƙasa Na Gusau

by Sulaiman
6 months ago
Gusau

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana matuƙar farin cikinsa bayan nasarar gudanar da gwajin saukar jirgi na farko a sabon Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa da ke Gusau.

 

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an bayyana cewa jirgin gwajin ya sauka da misalin ƙarfe 4:30 na yammacin ranar Lahadi, a wani lamari da aka bayyana a matsayin tarihi ga jihar.

ADVERTISEMENT
  • 2027: Cikin Ƴan APC Ya Ɗuri Ruwa Saboda Tasirin Makinde  – Ƙungiyar PDP
  • Kano Pillars Ta Doke Enyimba, Ta Matsa Gaba A Teburin Gasar NPFL

Sanarwar ta ƙara da cewa jirgin da aka yi amfani da shi, nau’in Bombardier Challenger 605, mallakin Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ne, wanda aka tura domin tantance inganci da shirye-shiryen filin jirgin kafin fara amfani da shi a hukumance.

 

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

A cewar sanarwar, wannan rana za ta kasance abin tunawa a tarihin Zamfara, kasancewar gwamnan ya shaida saukar jirgi na farko a filin jirgin da aka daɗe ana jira.

 

An bayyana cewa jirgin mai lambar rajista 5N-FGZ ya gudanar da gwaji na musamman domin tantance yadda filin jirgin zai iya karɓar manyan baƙi (VIP), musamman gabanin wasu muhimman zirga-zirga da ake sa ran yi a mako mai zuwa.

 

An kuma gudanar da wannan gwaji ne bisa tanade-tanaden dokokin sufurin jiragen sama na Nijeriya (Nigeria Civil Aviation Regulations), inda aka bi duk ƙa’idojin tsaro da aiki.

 

Kafin gudanar da gwajin, gwamnatin jihar ta nemi izini daga Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Nijeriya (NCAA), wadda ta bayar da amincewa ta musamman wato No Technical Objection (NTO) domin saukar jirgin a Gusau.

 

Haka kuma, an gudanar da aikin jirgin ne bisa tsarin Visual Flight Rules (VFR), wanda ke nufin an yi zirga-zirgar ne a tsakanin fitowar rana zuwa faɗuwarta, kamar yadda ƙa’ida ta tanada.

 

Wannan gagarumin ci gaba ya ƙara ɗaga darajar gwamnatin Gwamna Lawal, musamman idan aka yi la’akari da cewa tun bayan kafuwar Jihar Zamfara sama da shekaru 30 da suka gabata, ba ta taɓa samun filin jirgin sama irin wannan ba.

Gusau
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
PDP

Daƙile Taron Ƙasa Na Abuja: Ɓangaren PDP Ƙarƙashin Turaki Ya Caccaki Ɓangaren Wike 

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.