Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya ziyarci Hajiya Amina Rabe Abubakar, wacce aka ceto daga hannun ‘yan bindiga, wato matar marigayi tsohon Kakakin Hedikwatar Tsaro, Manjo Janar Rabe Abubakar.
Ya kai ziyarar ne a Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Katsina, inda take samun kulawar likitoci bayan ta ji rauni a lokacin ceto ta.
An ceto ta ne a wani samame da sojojin Operation FANSAN YAMMA suka kai, inda suka fafata da ‘yan bindiga tare da yin musayar wuta.
A yayin ziyarar da ya kai a ranar Litinin, gwamnan ya yaba wa jarumtar sojojin, yana mai cewa sun yi ƙwazo wajen yaƙi da ‘yan bindigar.
Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafa wa jami’an tsaro domin ƙarfafa yaƙi da ta’addanci da kuma tabbatar da zaman lafiya a Jihar Katsina.














Discussion about this post