Dakarun Sojin Nijeriya sun ƙwato makamai, abubuwan fashewa da wasu kayayyaki bayan sun fatattaki wasu da ake zargin ‘yan ta’addan Lakurawa ne a Jihar Kebbi.
An gudanar da aikin ne a ranar 14 ga watan Yuni a yankin Dogon Daji da ke ƙaramar hukumar Dandi, ƙarƙashin Sojojin Sashe na 2 na Operation FANSAN YAMMA.
Rahotanni sun ce sojojin sun tarwatsa ‘yan ta’addan, wanda ya tilasta musu tserewa daga maɓoyarsu.
Bayan haka sojojin sun bi diddginsu tare sa gano makamai da suka haɗa da rokoki (RPG), harsasai, abubuwan fashewa, babura biyu da ake zargin ‘yan ta’addan ke amfani da su wajen zirga-zirga, cajojin batiri, da sauran kayayyaki da suka bari.
Wata sanarwa daga Laftanar Kanal Olaniyi Osoba, mai magana da yawun rundunar sojin, ta ce babu wani soja da ya samu rauni a wannan farmaki.
Ya ce nasarar na nuna jajircewar rundunar wajen fatattakar ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga a yankin Arewa maso Yamma domin tabbatar da tsaro.
Sojojin sun kuma bayyana cewa za su ci gaba da ayyukansu domin hana masu laifi damar kai hare-hare da aikata laifuka a yankin.














Discussion about this post