• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Musanta Kashe Sama Da Miliyan 400 A Tafiye-tafiye

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Musanta Kashe Sama Da Miliyan 400 A Tafiye-tafiye
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal, ya karyata labarin cewa ya kashe sama da Naira miliyan 400 a tafiye-tafiye zuwa kasashen waje.

Wata jarida a Intanet ta ruwaito cewa Gwamna Dauda Lawal ya kashe Naira 170,276,294.31 wajen tafiye-tafiye na kasa da kasa, sai kuma Naira 221,567,094 na tafiye-tafiyen cikin gida sai kuma Naira 6,929,500.00 da suka shafi tafiye-tafiyen game harkokin tsaro cikin watanni uku.

  • Li Qiang Ya Halarci Taron Shugabannin G20 Da Aka Gudanar Ta Kafar Bidiyo
  • Da ÆŠumi-ÆŠumi: Kotun ÆŠaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Nasarar Gwamna Inuwa

Sai dai wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar a ranar Alhamis, ta ce wasu bata gari ne suka kirkiri labarin da gangan domin su bata sunan gwamnatin.

Ya bayyana cewa wannan ya samo asali ne daga kuskuren fassarar bayanan kasafin kudin jihar, inda ya kara da cewa kashi na daya da na biyu da na uku sun fada karkashin gwamnatin da ta shude.

Sanarwar ta kara da cewa: “Mun karanta wani rahoto da ke zargin Gwamna Dauda Lawal na kashe sama da Naira miliyan 400 wajen tafiye-tafiye zuwa kasashen waje. Wannan karya ce kuma yunkurin bata sunan gwamna ne.

Labarai Masu Nasaba

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

“Bin gaskiya da rikon amana su ne ginshikin gwamnatin Gwamna Dauda Lawal. Ana iya samun dukkan bayanan da suka dace game da gwamnatin Jihar Zamfara a shafin zamfara.gov.ng.

Sanarwar ta ce: “Rahoton ya yi kuskure wajen danganta kudaden da gwamnatin da ta gabata ta kashe da kashe kudaden da gwamnatinmu ta kashe. Gwamnatinmu ba ta taba daukar jami’an tsaro masu zaman kansu aiki ba. Don haka, muna mamakin yadda aka dangana mana kudaden da aka kashe a watan azumin ramadan da kuma kudaden bikin sallah.

“A matsayinmu na gwamnati, mun himmatu wajen tabbatar da gaskiya a duka ayyukanmu. Mun yi wa al’ummar Jihar Zamfara alkawarin kawo sauyi mai kyau, kuma mun kuduri aniyar cika wannan alkawari.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Zamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Yi Alkawarin Hada Hannu Da Milei Domin Kyautata Huldar Sin Da Argentina

Next Post

Kotu Ta Bayar Da Belin Tsohon Shugaban Hukumar KASCO Kan Miliyan 500

Related

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

3 hours ago
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
Manyan Labarai

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

4 hours ago
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820
Manyan Labarai

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

6 hours ago
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki
Manyan Labarai

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

7 hours ago
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

15 hours ago
Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo
Manyan Labarai

Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

17 hours ago
Next Post
Kotu Ta Bayar Da Belin Tsohon Shugaban Hukumar KASCO Kan Miliyan 500

Kotu Ta Bayar Da Belin Tsohon Shugaban Hukumar KASCO Kan Miliyan 500

LABARAI MASU NASABA

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya BuÆ™aci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

July 8, 2025
Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.