ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Na ɗaukar Matakai Don Rage Farashin Abinci Ta Hanyar Zuba Jari A Noma – Minista

by Sulaiman
1 year ago
Farashin Abinci

Gwamnatin Tarayya ta jaddada ƙudirin ta na rage farashin kayan abinci ta hanyar zuba jari mai yawa a fannin noma.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan a ranar Talata a Abuja yayin wani taron manema labarai da ya buɗe zaman bayar da rahoton ayyukan ministoci na shekarar 2025.

ADVERTISEMENT
  • Sin Ta Ayyana Matakan Bunkasa Harkokin Sayayya Da Zuba Jarin Waje
  • Al’ummomi 44 Sun Yi Zanga-zangar Rashin Samun Wutar Lantarki Na Tsawon Shekara Daya A Kwara

Ya jaddada cewa ko da yake gwamnati ba za ta ƙayyade farashin abinci ba, tana ƙoƙarin rage farashi ta hanyar haɓaka samar da amfanin gona.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Ya ce: “A baya, muna da wasu hukumomi da ke ƙayyade farashin kayan abinci, amma domin kasuwanci na ’yanci da bunƙasa harkokin noma, gwamnati ba ta ga dacewar ci gaba da hakan ba.

 

“Yanzu abin da gwamnati ke yi shi ne ta tabbatar da cewa ana samar da isassun kayan abinci, domin idan abu yana da yawa, farashin sa yana sauka da kan sa.”

 

Ministan ya kuma bayyana nasarorin da aka samu a fannin tsaro, inda ya ce a shekarar 2024 jami’an tsaro sun kashe ’yan ta’adda da ’yan bindiga sama da 8,000, sun kama mutum 11,600, tare da ƙwato makamai fiye da 10,000.

 

Ya tabbatar da cewa ƙoƙarin da ake yi yana sa hanyoyi na ƙara zama lafiya.

 

Ya ƙara da cewa, “Ko da yake har yanzu muna da aiki a gaba, hanyoyin mu sun fara zama mafi aminci.

“Hanyar Abuja zuwa Kaduna, wadda aka fi sani da rashin tsaro, tana daga cikin misalan da ke nuna irin cigaban da muke samu.

“Kamar yadda na faɗa, har yanzu akwai aiki da yawa a gaba, kuma ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba.

 

“Haka kuma, sama da mutum 8,000 da aka sace an kuɓutar da su cikin nasara.

“Za mu ci gaba da ƙoƙarin rage yawan waɗanda ake sacewa tare da bunƙasa nasarorin mu wajen hana laifuka, gano masu ma’aikatan su, da kuma hukunta su.”

 

Idris ya ƙara da cewa, bayan da Kotun Tarayya ta ayyana ƙungiyar Lakurawa a matsayin ’yan ta’adda, jami’an tsaro sun samu cikakken ikon amfani da ƙarfin da ya dace wajen murƙushe su.

 

Dangane da tattalin arziki, Ministan ya bayyana cewa sauye-sauyen da gwamnati ke aiwatarwa suna samar da ingantaccen sakamako, musamman cire tallafin fetur wanda ya hana asarar ɗaruruwan biliyoyin naira a kowace shekara.”

 

Ya jaddada cewa shigar da tsarin Electronic Foreign Exchange Matching System (EFEMS) a watan Disamba na 2023 ya inganta gaskiya a harkar canjin kuɗi, inda ya taimaka wajen warware bashin dalar Amurka da aka tara tun baya, da kuma dawo da ƙwarin gwiwar masu zuba jari.

 

“Makon jiya, Naira ta kai matsayi mafi ƙarfi cikin watanni takwas a kasuwar canji ta hukuma, yayin da jarin da ƙasashen waje ke zubawa a Kasuwar Hannun Jari ta Nijeriya ya ƙaru daga kashi 4 a tsakiyar 2023 zuwa kashi 16 a ƙarshen 2024.”

 

Ministan ya kuma bayyana cewa a shekarar 2024, Nijeriya ta zama ƙasa mafi jan hankalin masu zuba jari a ɓangaren man fetur da iskar gas a nahiyar Afrika, inda aka samu sama da dala biliyan 5.

 

Idris ya bayyana shekarar 2025 a matsayin shekara ta cigaba da gina nasarorin da aka samu a cikin wa’adin farko na mulkin Tinubu.

 

Ya ce za a gudanar da tarukan ministoci a duk mako na tsawon watanni uku masu zuwa domin tattauna nasarorin da aka samu a fannoni daban-daban.

 

Ya ce: “A cikin watanni uku masu zuwa, yayin da muke gab da cika shekaru biyu na mulkin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, za mu kawo ministoci zuwa wannan dandali a kowanne mako.

 

“Shekarar 2025 ita ce shekara ta ƙarfafa nasarorin da muka samu a cikin watanni 19 na farko na wannan gwamnati.

“Wannan zaman farko na 2025 dama ce ta tunatar da mu waɗannan nasarori da kuma tabbatar da irin cigaban da ake samu yayin da muke shirin shiga rabin wa’adin mulkin nan.”

Farashin Abinci
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Waɗanda Suka Sace Jigo A Jam’iyyar APC Sun Buƙaci A Biya Su Naira Miliyan 350

Waɗanda Suka Sace Jigo A Jam'iyyar APC Sun Buƙaci A Biya Su Naira Miliyan 350

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.