ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kebbi Ta Bayar Da Kwangilar Biliyan 3.8 Don Sake Gina Titunan Garin Yauri

by Umar Faruk
3 years ago
Kebbi

Gwamnatin Kebbi ta bayar da kwangilar Naira Biliyan 3.8 don sake gyaran titunan garin Yauri da ke masarautar Yauri a jihar.

Wannan dai ya yi daidai da shirin sabunta birane na Gwamna Nasir Idris wanda zai kai ga dukkan babban birnin jihar Kebbi, da Hedikwatar Masarautu hudu da kuma hedikwatar kananan hukumomi 21 na jihar.

  • Shin Wasan Kwaikwayon Na Zaben Kakakin Majalisar Wakilan Amurka Ta Kawo Karshe Ne? 
  • An Bude Iyakar Rafah Ga Wasu ‘Yan Kasashen Waje A Karon Farko

Kwamishinan Ayyuka da Sufuri, Alhaji Abdullahi Umar-Faruk ne ya bayyana hakan a Birnin Kebbi, a yayin da yake rattaba hannu kan yarjejeniyar kwangilar da wani kamfanin gine-gine na kasar Sin, China Zhounghou Nigeria Limited.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, “A yau, bisa tsarin shugabanci nagari na gwamnatin Gwamna Nasir Idris, mun taru ne domin shaida wata babbar nasara a tsakanin mutane da yawa masu zuwa, wato bikin rattaba hannu kan yarjejeniyar kwangila tsakanin gwamnatin jihar da Kamfanin kasar Sin Zhounghou. Nigeria Limited.

“kwangilar gyaran titunan garin Yauri ne, wanda ya hada da gyara da kuma sake gina wasu hanyoyi guda hudu da suka hada da, karamar hukumar Dawanau, titin kasuwa da ke kusa da Tashar Garkuwa, mahadar Garkan Dudu-Laberiya da ofishin ‘yansanda – Bankin Union baki daya. Za a kashe Naira Biliyan 3.8,” inji shi.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

A cewarsa, kwangilar za ta shafe kusan kilomita 5.2.

“A cikin watan Agusta, Gwamna Idris ya sake yin wata gagarumar nasara wajen bayar da kwangilar kammala ginin sakatariyar zamani a kan kudi Naira biliyan 10.5,” in ji shi.

“Muna kuma fatan kara tabbatar da cewa ma’aikatar ba za ta bar wani abu ba wajen tabbatar da cewa an kiyaye mafi ingancin aiki a tsawon watanni 18,” kwamishinan ya tabbatar.

Mista Wei Meng, wakilin kamfanin China Construction Company, China Zhounghou Nigeria Limited a takaice, ya tabbatar da cewa, kamfanin zai bi yarjejeniyar kwangila da kuma tabbatar da ingantaccen aiki.

Kebbi
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnatin Kebbi Ta Amince Da ₦2.07bn Alawus-alawus Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Maye Gurbin Mataimakinsa Da Ibrahim Augie A Zaɓen 2027
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Matashi Ya Shiga Hannu Kan Zargin Wulaƙanta Alƙur’ani A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Miƙa Yara 5 Da Aka Ceto Daga Hannun Masu Safarar Mutane Ga Iyayensu

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Next Post
Baje Kolin CIIE Ya Samu Yabo Daga Sassan Kasa Da Kasa A Matsayin Dandalin Bunkasa Hadin Gwiwa Da Ci Gaba

Baje Kolin CIIE Ya Samu Yabo Daga Sassan Kasa Da Kasa A Matsayin Dandalin Bunkasa Hadin Gwiwa Da Ci Gaba

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.