ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Ni Da Shirin Komawa PRP – Gwamnan Bauchi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
7 months ago
Bala Mohammed

Gwamnan jihar Bauchi ta ƙaryata batun da ke cewa, “gwamnan jjihar Bauchi Bala Muhammad na shirin ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar PRP”.

Wata sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Mukhtar Gidado ya fitar a ranar Laraba, ya misalta zargin da cewa marar tushe balle makama, ya tabbatar da cewa gwamnan bai taɓa niyyar ficewa a PDP wai don ya shiga cikin PRP ba.

  • ‘Yan Majalisa Sun Gayyaci Gwamnan CBN Kan Rashin Tura Naira Tiriliyan 16 Ga Asusun Gwamnati
  • ‘Yan Majalisa Sun Gayyaci Gwamnan CBN Kan Rashin Tura Naira Tiriliyan 16 Ga Asusun Gwamnati

“Hankulanmu sun karkata kan wani bayanin da aka danganta da sakataren jam’iyyar PRP na jihar Bauchi da ke zargin cewa jam’iyyar ta nuna rashin amincewarta da yunƙurin dawowar gwamna Bala Muhammad zuwa cikinta. Inda wai ta ke nuna ba ta maraba da dawowar nasa.

ADVERTISEMENT

“A zahirin gaskiya, kamatuwa ma ya yi mu yi buris da irin wannan zargin ba tare da an kula ba domin fita sha’anin masu neman hankali ya karkata kansu. Amma, yin shirun zai sanya ƙaryar ta ci gaba da sanya shakku a zukatan wasu, don haka akwai buƙatar fayyace zare da abawa,” sanarwar ta shaida.

Sanarwar ta ce gabaki ɗaya bayanin da aka danganta da jami’in jam’iyyar PRP babu wani abu mai kama da gaskiya a ciki illa tunani ne kawai na wanda ya fitar da batun.

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

“Muna son mu tabbatar wa jama’a cewa gwamnan Bala Mohammed bai taɓa tunanin ficewa daga PDP domin ya shiga wata jam’iyyar siyasa balle ma wai PRP, ba” Gidado ya zayyana.

Ya ƙara da cewa gwamna Bala Muhammad wanda shi ne shugaban ƙungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP ya kasance na gaba-gaba wajen tabbatar da haɗin kai da ci gaban jam’iyyar PDP duk da ƙalubalen da suke fuskanta daga masu adawa da demokraɗiyya masu neman mayar da ƙasar nan tsarin jam’iyya guda tak.

Gidado ya ƙara da cewa ƙoƙarin gwamna Bala Muhammad ya karaɗe sassa daban-daban daga jihar zuwa wajenta wanda ya kayar da manyan jam’iyyu a manyan zaɓuka guda biyu bisa nagarta da cancantarsa.

Sanarwar ta ce a halin yanzu jihar Bauchi ta samu ci gaba fiye da yadda ake tunani dukka a ƙarƙashin gwamnatin Bala Muhammad don haka babu wani dalilin da wata jam’iyya za ta nemi wawaitar da hankalin jama’an jihar.

Ya nuna cewa gwamna Bala yana da cikakken ‘yancin zaɓar inda zai sanya gaba a siyasance don haka ne ya nemi masu yaɗa jita-jita da su daina.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan
  • Sulaiman
    Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
  • Sulaiman
    An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai
  • Sulaiman
    Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

MASU ALAKA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Next Post
An Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa Na Sin Da Afrika Kan Kare Hakkin Dan Adam

An Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa Na Sin Da Afrika Kan Kare Hakkin Dan Adam

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.