ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Ni Da Shirin Komawa PRP – Gwamnan Bauchi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
7 months ago
Bala Mohammed

Gwamnan jihar Bauchi ta ƙaryata batun da ke cewa, “gwamnan jjihar Bauchi Bala Muhammad na shirin ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar PRP”.

Wata sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Mukhtar Gidado ya fitar a ranar Laraba, ya misalta zargin da cewa marar tushe balle makama, ya tabbatar da cewa gwamnan bai taɓa niyyar ficewa a PDP wai don ya shiga cikin PRP ba.

  • ‘Yan Majalisa Sun Gayyaci Gwamnan CBN Kan Rashin Tura Naira Tiriliyan 16 Ga Asusun Gwamnati
  • ‘Yan Majalisa Sun Gayyaci Gwamnan CBN Kan Rashin Tura Naira Tiriliyan 16 Ga Asusun Gwamnati

“Hankulanmu sun karkata kan wani bayanin da aka danganta da sakataren jam’iyyar PRP na jihar Bauchi da ke zargin cewa jam’iyyar ta nuna rashin amincewarta da yunƙurin dawowar gwamna Bala Muhammad zuwa cikinta. Inda wai ta ke nuna ba ta maraba da dawowar nasa.

ADVERTISEMENT

“A zahirin gaskiya, kamatuwa ma ya yi mu yi buris da irin wannan zargin ba tare da an kula ba domin fita sha’anin masu neman hankali ya karkata kansu. Amma, yin shirun zai sanya ƙaryar ta ci gaba da sanya shakku a zukatan wasu, don haka akwai buƙatar fayyace zare da abawa,” sanarwar ta shaida.

Sanarwar ta ce gabaki ɗaya bayanin da aka danganta da jami’in jam’iyyar PRP babu wani abu mai kama da gaskiya a ciki illa tunani ne kawai na wanda ya fitar da batun.

LABARAI MASU NASABA

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

“Muna son mu tabbatar wa jama’a cewa gwamnan Bala Mohammed bai taɓa tunanin ficewa daga PDP domin ya shiga wata jam’iyyar siyasa balle ma wai PRP, ba” Gidado ya zayyana.

Ya ƙara da cewa gwamna Bala Muhammad wanda shi ne shugaban ƙungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP ya kasance na gaba-gaba wajen tabbatar da haɗin kai da ci gaban jam’iyyar PDP duk da ƙalubalen da suke fuskanta daga masu adawa da demokraɗiyya masu neman mayar da ƙasar nan tsarin jam’iyya guda tak.

Gidado ya ƙara da cewa ƙoƙarin gwamna Bala Muhammad ya karaɗe sassa daban-daban daga jihar zuwa wajenta wanda ya kayar da manyan jam’iyyu a manyan zaɓuka guda biyu bisa nagarta da cancantarsa.

Sanarwar ta ce a halin yanzu jihar Bauchi ta samu ci gaba fiye da yadda ake tunani dukka a ƙarƙashin gwamnatin Bala Muhammad don haka babu wani dalilin da wata jam’iyya za ta nemi wawaitar da hankalin jama’an jihar.

Ya nuna cewa gwamna Bala yana da cikakken ‘yancin zaɓar inda zai sanya gaba a siyasance don haka ne ya nemi masu yaɗa jita-jita da su daina.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba
  • Sulaiman
    Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)
  • Sulaiman
    Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
  • Sulaiman
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

MASU ALAKA

Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje
Labarai

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

June 26, 2026
Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

June 26, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya
Labarai

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

June 26, 2026
Next Post
An Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa Na Sin Da Afrika Kan Kare Hakkin Dan Adam

An Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa Na Sin Da Afrika Kan Kare Hakkin Dan Adam

LABARAI MASU NASABA

Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

June 26, 2026
Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

June 26, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

June 26, 2026
Noma

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.