ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Ni Da Shirin Komawa PRP – Gwamnan Bauchi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
7 months ago
Bala Mohammed

Gwamnan jihar Bauchi ta ƙaryata batun da ke cewa, “gwamnan jjihar Bauchi Bala Muhammad na shirin ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar PRP”.

Wata sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Mukhtar Gidado ya fitar a ranar Laraba, ya misalta zargin da cewa marar tushe balle makama, ya tabbatar da cewa gwamnan bai taɓa niyyar ficewa a PDP wai don ya shiga cikin PRP ba.

  • ‘Yan Majalisa Sun Gayyaci Gwamnan CBN Kan Rashin Tura Naira Tiriliyan 16 Ga Asusun Gwamnati
  • ‘Yan Majalisa Sun Gayyaci Gwamnan CBN Kan Rashin Tura Naira Tiriliyan 16 Ga Asusun Gwamnati

“Hankulanmu sun karkata kan wani bayanin da aka danganta da sakataren jam’iyyar PRP na jihar Bauchi da ke zargin cewa jam’iyyar ta nuna rashin amincewarta da yunƙurin dawowar gwamna Bala Muhammad zuwa cikinta. Inda wai ta ke nuna ba ta maraba da dawowar nasa.

ADVERTISEMENT

“A zahirin gaskiya, kamatuwa ma ya yi mu yi buris da irin wannan zargin ba tare da an kula ba domin fita sha’anin masu neman hankali ya karkata kansu. Amma, yin shirun zai sanya ƙaryar ta ci gaba da sanya shakku a zukatan wasu, don haka akwai buƙatar fayyace zare da abawa,” sanarwar ta shaida.

Sanarwar ta ce gabaki ɗaya bayanin da aka danganta da jami’in jam’iyyar PRP babu wani abu mai kama da gaskiya a ciki illa tunani ne kawai na wanda ya fitar da batun.

LABARAI MASU NASABA

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

“Muna son mu tabbatar wa jama’a cewa gwamnan Bala Mohammed bai taɓa tunanin ficewa daga PDP domin ya shiga wata jam’iyyar siyasa balle ma wai PRP, ba” Gidado ya zayyana.

Ya ƙara da cewa gwamna Bala Muhammad wanda shi ne shugaban ƙungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP ya kasance na gaba-gaba wajen tabbatar da haɗin kai da ci gaban jam’iyyar PDP duk da ƙalubalen da suke fuskanta daga masu adawa da demokraɗiyya masu neman mayar da ƙasar nan tsarin jam’iyya guda tak.

Gidado ya ƙara da cewa ƙoƙarin gwamna Bala Muhammad ya karaɗe sassa daban-daban daga jihar zuwa wajenta wanda ya kayar da manyan jam’iyyu a manyan zaɓuka guda biyu bisa nagarta da cancantarsa.

Sanarwar ta ce a halin yanzu jihar Bauchi ta samu ci gaba fiye da yadda ake tunani dukka a ƙarƙashin gwamnatin Bala Muhammad don haka babu wani dalilin da wata jam’iyya za ta nemi wawaitar da hankalin jama’an jihar.

Ya nuna cewa gwamna Bala yana da cikakken ‘yancin zaɓar inda zai sanya gaba a siyasance don haka ne ya nemi masu yaɗa jita-jita da su daina.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
  • Sulaiman
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
  • Sulaiman
    Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita
  • Sulaiman
    Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

MASU ALAKA

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci
Labarai

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Labarai

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda
Labarai

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Next Post
An Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa Na Sin Da Afrika Kan Kare Hakkin Dan Adam

An Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa Na Sin Da Afrika Kan Kare Hakkin Dan Adam

LABARAI MASU NASABA

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.