Gwamnan jihar Bauchi ta ƙaryata batun da ke cewa, “gwamnan jjihar Bauchi Bala Muhammad na shirin ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar PRP”.
Wata sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Mukhtar Gidado ya fitar a ranar Laraba, ya misalta zargin da cewa marar tushe balle makama, ya tabbatar da cewa gwamnan bai taɓa niyyar ficewa a PDP wai don ya shiga cikin PRP ba.
- ‘Yan Majalisa Sun Gayyaci Gwamnan CBN Kan Rashin Tura Naira Tiriliyan 16 Ga Asusun Gwamnati
- ‘Yan Majalisa Sun Gayyaci Gwamnan CBN Kan Rashin Tura Naira Tiriliyan 16 Ga Asusun Gwamnati
“Hankulanmu sun karkata kan wani bayanin da aka danganta da sakataren jam’iyyar PRP na jihar Bauchi da ke zargin cewa jam’iyyar ta nuna rashin amincewarta da yunƙurin dawowar gwamna Bala Muhammad zuwa cikinta. Inda wai ta ke nuna ba ta maraba da dawowar nasa.
“A zahirin gaskiya, kamatuwa ma ya yi mu yi buris da irin wannan zargin ba tare da an kula ba domin fita sha’anin masu neman hankali ya karkata kansu. Amma, yin shirun zai sanya ƙaryar ta ci gaba da sanya shakku a zukatan wasu, don haka akwai buƙatar fayyace zare da abawa,” sanarwar ta shaida.
Sanarwar ta ce gabaki ɗaya bayanin da aka danganta da jami’in jam’iyyar PRP babu wani abu mai kama da gaskiya a ciki illa tunani ne kawai na wanda ya fitar da batun.
“Muna son mu tabbatar wa jama’a cewa gwamnan Bala Mohammed bai taɓa tunanin ficewa daga PDP domin ya shiga wata jam’iyyar siyasa balle ma wai PRP, ba” Gidado ya zayyana.
Ya ƙara da cewa gwamna Bala Muhammad wanda shi ne shugaban ƙungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP ya kasance na gaba-gaba wajen tabbatar da haɗin kai da ci gaban jam’iyyar PDP duk da ƙalubalen da suke fuskanta daga masu adawa da demokraɗiyya masu neman mayar da ƙasar nan tsarin jam’iyya guda tak.
Gidado ya ƙara da cewa ƙoƙarin gwamna Bala Muhammad ya karaɗe sassa daban-daban daga jihar zuwa wajenta wanda ya kayar da manyan jam’iyyu a manyan zaɓuka guda biyu bisa nagarta da cancantarsa.
Sanarwar ta ce a halin yanzu jihar Bauchi ta samu ci gaba fiye da yadda ake tunani dukka a ƙarƙashin gwamnatin Bala Muhammad don haka babu wani dalilin da wata jam’iyya za ta nemi wawaitar da hankalin jama’an jihar.
Ya nuna cewa gwamna Bala yana da cikakken ‘yancin zaɓar inda zai sanya gaba a siyasance don haka ne ya nemi masu yaɗa jita-jita da su daina.














