ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Haɗin Gwiwar Sin Da Majalisar Ɗinkin Duniya Na Da Tasiri Ga Makomar Zaman Lafiyar Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

Ƙasar Sin a matsayinta na mamba a ƙungiyar ta duniya wato Majalisar Ɗinkin Duniya, ta ci gaba da tsayawa tsayin daka wajen ba da shawararta na tabbatar da ra’ayin bangarori daban-daban na gaskiya, kuma tana son taƙaita rashin daidaiton tattalin arziki da zamantakewar al’umma da ke illa ga yankunan duniya. Inganta haɗin gwiwa tsakanin Sin da MDD wajen samun ci gaba mai ɗorewa, da sauyin yanayi, da kirkire-kirkire na zamani, da kare hakkin dan Adam, wani babban mataki ne na tabbatar da daidaito da dawwamar zaman lafiyar a duniya. 

Ƙasar Sin na ci gaba da ciyar da wakilcin yankin kudu na duniya gaba ta hanyar faɗaɗa shirinta na BRICS da shirinta na shawarar ziri ɗaya da hanya ɗaya (BRI), tare da samar da kuɗaɗe masu sassaucin ƙa’idoji ga ƙasashe masu ƙaramin ƙarfi, da ƙara ƙarfin muradun ci gaba mai ɗorewa (SDGs) a ƙasashen Afirka da dama.

  • Rikicin Gabar Yammacin Kogin Jordan: Falasdinu Ta Kawo Karshen Hulda Da Isra’ila

Dangane da manufofin Majalisar Ɗinkin Duniya, BRI na ci gaba da tallafa wa ɗimbin ƙasashe masu tasowa a yunkurinsu na samun ci gaba mai ɗorewa, wanda Majalisar Ɗinkin Duniya ke kallonsa a matsayin wani muhimmin jagoranci kan ci gaban fasaha.

ADVERTISEMENT

Tuni MDD ta yi gargadin cewa, alfanun irin wannan sauyi ya karkata sosai zuwa ga ƙasashe masu arziki, yana mai jaddada muhimmancin kiyaye ƙarin “abokan haɗin gwiwa” da ƙasar Sin, don taimakawa wajen cimma burin SDG.

A matsayinta na ƙasa mai tasowa mafi girma, Sin ta fahimci muhimmancin jagoranci kan kare hakkin dan Adam da daidaiton jinsi. A gun taron kwamitin kare hakkin bil adama na MDD karo na 53 da aka gudanar, ƙasar Sin ta yi na’am da kiraye-kirayen da ƙasashe kusan 80 suka yi na ƙarfafa haɗin kai, maimakon rarrabuwar kawuna, wajen tinkarar ƙalubalen hakkin dan Adam.

LABARAI MASU NASABA

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

Hakazalika, ra’ayin Sin game da ’yancin ɗan adam ya samar da gagarumar nasara a kan yaƙi da matsananciyar talauci, musamman ga ƙasar da ta kai kusan kashi biyar na al’ummar duniya, bisa la’akari da irin wannan fa’ida, ƙasar Sin ta bude wani sabon salo na haɗin gwiwar raya ƙasa tare da MDD, wanda ya ƙunshi shigar da ’yan kasuwa sama da 650 na ƙasar Sin a cikin yarjejeniyar duniya ta MDD kan ’yancin dan Adam, da samar da ayyukan yi, da muhalli da yaƙi da cin hanci da rashawa.

Yayin da ake fuskantar barazanar koma bayan tattalin arziki, da rashin tabbas na ci gaba, da rikice-rikice masu yawa, yana da matuƙar muhimmanci ga MDD da Sin su zurfafa alaƙa, da magance giɓin da ake samu wajen zaman lafiya, da ci gaba da shugabanci.

Shirin raya ƙasa da ƙasa (GDI) da ƙasar Sin ke jagoranta, shi ma wani kyakkyawan misali ne na ci gaban da aka samu tare. Majalisar Ɗinkin Duniya ta tallafa wa asusun haɗin gwiwar kudu-maso-kudu na GDI, albarkatun da ke baiwa ƙasashe damar shawo kan matsalolin kuɗi da kuma kawo cikas ga maƙasudan ci gaba mai ɗorewa.

A yayin da ɓangarorin biyu ke ƙoƙarin yin haɗin gwiwa kan ayyukan sauyin yanayi a duniya, goyon bayan da ƙasar Sin ta bayar na haɗin gwiwa a fannin makamashi mai tsafta a duniya, wata shaida ce ta yaƙi da rikice-rikicen da ake fuskanta.

Ƙarfafa haɗin gwiwa tare da Sin a fannoni daban-daban, ya sake jadadda wannan batu na cewa, “Haɗin gwiwar Sin da Majalisar Ɗinkin Duniya na da tasiri ga makomar zaman lafiyar duniya”. (Yahaya Babs)

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki
Daga Birnin Sin

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

July 12, 2026
Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

July 12, 2026
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

July 12, 2026
Next Post
Gwamnan Kebbi Ya Kori Hadiminsa Kan Wallafa Wani Sako A Kafafen Sada Zumunta

Gwamnan Kebbi Ya Kori Hadiminsa Kan Wallafa Wani Sako A Kafafen Sada Zumunta

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

July 13, 2026
Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar da Matatar Sarrafa Ma’adanin Lithium Ta $200m A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar da Matatar Sarrafa Ma’adanin Lithium Ta $200m A Zamfara

July 13, 2026
Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa

Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa

July 13, 2026
Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

July 12, 2026
Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

July 12, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

July 12, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.