Wani babban masani a kasar Habasha ya bayyana cewa, kasar tana sa ran cin gajiyar katafariyar kasuwar kayan lambu ta kasar Sin, inda za ta yi amfani da damar da gwamnatin Sin ta bayar ta manufar soke harajin kwastam ga kasashe 53 na Afirka masu alakar diflomasiyya da ita.
Masanin, Tewodros Zewdie, babban daraktan kungiyar masu fitar da kayan lambu ta kasar Habasha, ya ce tagomashin wannan manufa ta soke harajin kwastam na kasar Sin zai kara inganta fitar da kayan lambu na Habasha sosai kuma ya karfafa tsarin kasuwancinta gaba daya.
A wata hirar da ya yi da kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua ranar Asabar da ta gabata, Zewdie ya bayyana cewa, kasuwar kasar Sin na samar da daruruwan miliyoyin masu sayen kayan da ake fitarwa daga Afirka, kuma tana daya daga cikin muhimman masu taka rawar gani a masana’antar kayan lambu, don haka za ta taimaka mana wajen fadada kasuwar da muke kai kayanmu da kuma cikakken bude fikirar da kasar Habasha take da ita.”
Ya kara da cewa, “Abin farin ciki shi ne, muna da kamfanin jiragen sama na Habasha, wanda yake gudanar zirga-zirgar jirage fiye da 40 zuwa kasar Sin duk mako. Don haka, akwai wadatattun harkokin jigila. Damammakin da ake da su a kasuwar Sin za su taimaka mana wajen kara samun kudaden waje, da kuma kirkiro da guraben ayyukan yi masu kyau ga dubban Habashawa da ke cikin kasa.” (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post