Kwamitin Shirya Gasar Cin Kofin Sarkin Gombe da ake yiwa lakabi da Emir Cup ya tabbatar da cewa an kammala dukkan shirye-shirye domin samun nasarar shirya gasar ta wannan shekarar, inda ake dab da fara buga gasar a babban filin wasa na Pantami a jihar Gombe.
An shirya bikin bude gasar cin kofin kwallon kafar a ranar Asabar, 13 ga watan Yunin wannan shekarar da karfe 3 na yamma, wanda ake fatan zai zama wata hanyar habaka hadin kai da karfafa zumunta tsakanin matasa a fadin Jihar Gombe, gasar na daga cikin manyan kofuna da ake bugawa a Arewacin Nijeriya inda ake hada manyan masarautu waje daya.
Masu shirya gasar sunce suna ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen zakulo hazikan yan wasa da kuma karfafa matasa ta hanyar samar da wani dandamali da yan wasan zasu nuna kwazonsu da kwarewasu a fagen kwallon kafa, kuma ya zama wani waje da za’a samar da wadanda zasu wakilci Nijeriya a matakin kasa da kasa a nan gaba.
Tsohon Shugaban kungiyar kwallon kafa ta Jihar Gombe, Alhaji Ahmed Shuaibu Gara Gombe ne ke daukar nauyin gasar, wadda ake sa ran manyan mutane, ciki har da sarakunan gargajiya, jami’an gwamnati, masu gudanar da kungiyoyin kwallon kafa daga ciki da wajen Jihar Gombe, za su halarci bikin bude gasar, masu shirya gasar sunyi kira ga masoyan kwallon kafa, shugabannin al’umma da masu ruwa da tsaki da su goyi bayan gasar, da suka bayyana a matsayin muhimmiyar hanya ga hadin kai tsakanin jama’a da kuma ci gaban taurarin kwallon kafa.















Discussion about this post