ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwa Da Sin Na Ingiza Ci Gaban Kasashen Afirka, In Ji Wani Kwararre

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

Kwararre a fannin tsara manufofi dan kasar Habasha, Farfesa Costantinos Berhutesfa Costantinos, ya ce hadin gwiwa da kasar Sin ya bunkasa ci gaban kasashen Afirka, yayin da bikin baje kolin tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Afirka karo na 3 ya kara ingiza saurin ci gaban da nahiyar ke samu.

Yayin wata tattaunawa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua a baya bayan nan, Farfesa Costantinos, wanda ke koyarwa a jami’ar Addis Ababan kasar Habasha, ya ce baje kolin wanda ya gudana tsakanin ranaikun Alhamis zuwa Lahadin nan a birnin Changsha fadar mulkin lardin Hunan na tsakiyar kasar Sin, zai karfafa fadadar alakar cinikayya da tattalin arziki tsakanin Sin da kasashen Afirka, tare da kara tabbatar da matsayin kasar Sin, na kasancewa muhimmiyar abokiyar cudanyar kasashen na Afirka.

  • Jimillar Yarjeniyoyi Da Bangarori Daban Daban Suka Daddale Yayin Taron Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Kasashen Afirka Ta Kai 120

Baje kolin na bana, mai taken “Ci gaban bai daya domin makomar bai daya ga kowa” ya samu halartar wakilai daga kasashen Afirka 53, da wasu hukumomin kasa da kasa da dama. Kaza lika adadin masu baje hajoji yayin baje kolin na bana ya kai 1,500, adadin da ya karu da kaso 70 bisa dari kan wanda ya gabace shi.

ADVERTISEMENT

A cewar shaihun malamin, yanzu haka, kasar Sin ce abokiyar cinikayyar Afirka mafi girma, kuma kasa ta hudu a girman zuba jari a nahiyar. Har ila yau, alkaluma sun nuna cewa, a shekarar 2022, cudanyar cinikayya tsakanin Sin da kasashen nahiyar ta kai darajar dalar Amurka biliyan 282. Kuma cikin watanni hudun farkon shekarar nan, adadin sabbin kudaden jarin kai tsaye da Sin ta zuba a kasashen Afirka ya kai dala biliyan 1.38, adadin da ya karu da kaso 24 bisa dari a shekara.

A daya bangaren kuma, tasirin Sin a fannin bunkasar tattalin arzikin kasashen Afirka, ya wuce batun samar da ababen more rayuwa, inda ya kutsa zuwa sauran muhimman fannonin samar da ci gaba. Gina yankunan raya tattalin arziki na musamman da Sin ta yi a kasashen nahiyar da dama, shi ma ya samar da karin damar bunkasa fannin masana’antun nahiyar Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Farfesa Costantinos ya kara da cewa, kasashen Afirka da kamfanonin su, za su iya cin karin gajiya daga baje kolin, musamman a fannin bunkasa ayyukan masana’antu, ta yadda za su kara shiga kasuwannin Sin, da ma na sauran sassan duniya. (Saminu Alhassan)

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Me Ya Sa Amurka Ta Sake Komawa UNESCO Bayan Da Ta Sha Ficewa Daga Hukumar?

Me Ya Sa Amurka Ta Sake Komawa UNESCO Bayan Da Ta Sha Ficewa Daga Hukumar?

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.