ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin Venezuela Ta’asa Ce Da Amurka Ke Tafkawa Tun Bayan Yakin Duniya Na Biyu

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Venezuela

Ta’asar da Amurka ta tafka ta zuwa cikin Venezuela, kasa mai cin gashin kanta, ta cafke shugaban kasa mai cikakken iko da nufin gurfanar da shi a kotun kasarta, daya ne daga cikin munanan abubuwan da kasar take gadar wa duniya tun bayan yakin duniya na biyu.

Amurka ta yi kaurin suna wajen fakewa da guzuma ta harbi karsana a kasashe daban-daban a bayyane da kuma a boye, wadanda ake ganin sun yi hannun riga da manufofinta na ci da gumin wasu.

A shekarar 1953, hukumar leken asiri ta Amurka (CIA) ta mara baya ga kifar da firaministan Iran Mohammad Mossadegh bayan ya mayar da iko da arzikin man kasar zuwa ga kasarsa. Shekara guda bayan nan, hakan ya sake faruwa a Guatemala inda aka tumbuke zababben shugaban kasar Jacob Arbenz, dukka da sunan kare ’yancin jama’a.

ADVERTISEMENT

A shekarar 1961, Amurka ta farmaki kasar Cuba, a 1983 kuma ta kai mamaya a kasar Grenada wanda Majalisar Dinkin Duniya ta fito fili ta yi tir da hakan. Kazalika a 1989, ta kai hare-hare a Panama tare da tumbuke shugaban kasar Manuel Noriega bayan haddasa dimbin asarar rayukan fararen hula. Taho-taho har aka tsallako karni na 21, Amurka ba ta daina ta’asarta ba. Ta yi gaban kanta tare da wancakalar da dokokin kasa da kasa ta afka wa Iraqi a 2003, ta kuma zama kanwa-uwar-gamin wargaza kwanciyar hankalin Libiya a karkashin NATO a 2011. Wadannan duka wasu misalai ne kawai daga ta’asar da take tafkawa, baya ga yakin sunkuru na hana sakat a wasu kasashe.

Yanayin kasa da kasa ya riga ya shiga cikin wani mawuyacin hali da aka dade ba a ga irinsa ba sakamakon miyagun dabi’un Amurka, kuma galibi kamar yadda masharhanta da dama ke fada, ba don komai ba ne illa kare matsayinta na babakere a duniya. Harin da Amurka ta kai wa Venezuela ya kara tsananta fargabar al’umma a wasu yankuna da ake fama da rikice-rikice domin kar hakan ya zama silar murkushe kananan kasashen da ake rikici da su.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

A daya daga cikin jawabansa, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya taba bayyana cewa, bai kamata a mayar da duniyarmu ta karni 21 mai wayewar kai ta dan’adam ta koma rayuwa irin ta namun daji ba, watau babba ya rika farautar mai rauni.

Hakika, lokaci ya yi da za a amsa kiraye-kirayen kasar Sin na hada karfi da karfe wajen tabbatar da bin dokokin kasa da kasa a karkashin ikon Majalisar Dinkin Duniya. Harin da Amurka ta kai wa Venezuela ya wuce wani abu na yankin Latin da Caribbean kawai, gargadi ne da an kararwa game da halin da duniya ke ciki na cin zalin daga kasar da ke ganin babu mai nuna mata isa. Yana gaya wa duniya cewa har yanzu za a iya yin hakan a kwana lafiya, kuma bin dokokin kasa da kasa ba tilas ba ne zabi ne ga manyan kasashe.

Idan abin ya ci gaba a haka ba tare da an ja masa burki ba, tsarin duniya da ke cikin mawuyacin hali zai iya rugujewa, musamman ma ganin cewa, bayan Venezuela, yanzu haka Amurka ta maida hankali ga kwace yankin Greenland na kasar Denmark, lamarin da zai sake haifar da mummunan rudani a duniya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Venezuela
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Venezuela
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
An Kama Mutane 8 Da Ake Zargi Da Hannu A Harin Ƙunar Baƙin Wake A Masallacin Borno

An Kama Mutane 8 Da Ake Zargi Da Hannu A Harin Ƙunar Baƙin Wake A Masallacin Borno

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.