ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin Venezuela Ta’asa Ce Da Amurka Ke Tafkawa Tun Bayan Yakin Duniya Na Biyu

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Venezuela

Ta’asar da Amurka ta tafka ta zuwa cikin Venezuela, kasa mai cin gashin kanta, ta cafke shugaban kasa mai cikakken iko da nufin gurfanar da shi a kotun kasarta, daya ne daga cikin munanan abubuwan da kasar take gadar wa duniya tun bayan yakin duniya na biyu.

Amurka ta yi kaurin suna wajen fakewa da guzuma ta harbi karsana a kasashe daban-daban a bayyane da kuma a boye, wadanda ake ganin sun yi hannun riga da manufofinta na ci da gumin wasu.

A shekarar 1953, hukumar leken asiri ta Amurka (CIA) ta mara baya ga kifar da firaministan Iran Mohammad Mossadegh bayan ya mayar da iko da arzikin man kasar zuwa ga kasarsa. Shekara guda bayan nan, hakan ya sake faruwa a Guatemala inda aka tumbuke zababben shugaban kasar Jacob Arbenz, dukka da sunan kare ’yancin jama’a.

ADVERTISEMENT

A shekarar 1961, Amurka ta farmaki kasar Cuba, a 1983 kuma ta kai mamaya a kasar Grenada wanda Majalisar Dinkin Duniya ta fito fili ta yi tir da hakan. Kazalika a 1989, ta kai hare-hare a Panama tare da tumbuke shugaban kasar Manuel Noriega bayan haddasa dimbin asarar rayukan fararen hula. Taho-taho har aka tsallako karni na 21, Amurka ba ta daina ta’asarta ba. Ta yi gaban kanta tare da wancakalar da dokokin kasa da kasa ta afka wa Iraqi a 2003, ta kuma zama kanwa-uwar-gamin wargaza kwanciyar hankalin Libiya a karkashin NATO a 2011. Wadannan duka wasu misalai ne kawai daga ta’asar da take tafkawa, baya ga yakin sunkuru na hana sakat a wasu kasashe.

Yanayin kasa da kasa ya riga ya shiga cikin wani mawuyacin hali da aka dade ba a ga irinsa ba sakamakon miyagun dabi’un Amurka, kuma galibi kamar yadda masharhanta da dama ke fada, ba don komai ba ne illa kare matsayinta na babakere a duniya. Harin da Amurka ta kai wa Venezuela ya kara tsananta fargabar al’umma a wasu yankuna da ake fama da rikice-rikice domin kar hakan ya zama silar murkushe kananan kasashen da ake rikici da su.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

A daya daga cikin jawabansa, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya taba bayyana cewa, bai kamata a mayar da duniyarmu ta karni 21 mai wayewar kai ta dan’adam ta koma rayuwa irin ta namun daji ba, watau babba ya rika farautar mai rauni.

Hakika, lokaci ya yi da za a amsa kiraye-kirayen kasar Sin na hada karfi da karfe wajen tabbatar da bin dokokin kasa da kasa a karkashin ikon Majalisar Dinkin Duniya. Harin da Amurka ta kai wa Venezuela ya wuce wani abu na yankin Latin da Caribbean kawai, gargadi ne da an kararwa game da halin da duniya ke ciki na cin zalin daga kasar da ke ganin babu mai nuna mata isa. Yana gaya wa duniya cewa har yanzu za a iya yin hakan a kwana lafiya, kuma bin dokokin kasa da kasa ba tilas ba ne zabi ne ga manyan kasashe.

Idan abin ya ci gaba a haka ba tare da an ja masa burki ba, tsarin duniya da ke cikin mawuyacin hali zai iya rugujewa, musamman ma ganin cewa, bayan Venezuela, yanzu haka Amurka ta maida hankali ga kwace yankin Greenland na kasar Denmark, lamarin da zai sake haifar da mummunan rudani a duniya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Venezuela
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Venezuela
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
An Kama Mutane 8 Da Ake Zargi Da Hannu A Harin Ƙunar Baƙin Wake A Masallacin Borno

An Kama Mutane 8 Da Ake Zargi Da Hannu A Harin Ƙunar Baƙin Wake A Masallacin Borno

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.