ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin Venezuela Ta’asa Ce Da Amurka Ke Tafkawa Tun Bayan Yakin Duniya Na Biyu

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Venezuela

Ta’asar da Amurka ta tafka ta zuwa cikin Venezuela, kasa mai cin gashin kanta, ta cafke shugaban kasa mai cikakken iko da nufin gurfanar da shi a kotun kasarta, daya ne daga cikin munanan abubuwan da kasar take gadar wa duniya tun bayan yakin duniya na biyu.

Amurka ta yi kaurin suna wajen fakewa da guzuma ta harbi karsana a kasashe daban-daban a bayyane da kuma a boye, wadanda ake ganin sun yi hannun riga da manufofinta na ci da gumin wasu.

A shekarar 1953, hukumar leken asiri ta Amurka (CIA) ta mara baya ga kifar da firaministan Iran Mohammad Mossadegh bayan ya mayar da iko da arzikin man kasar zuwa ga kasarsa. Shekara guda bayan nan, hakan ya sake faruwa a Guatemala inda aka tumbuke zababben shugaban kasar Jacob Arbenz, dukka da sunan kare ’yancin jama’a.

ADVERTISEMENT

A shekarar 1961, Amurka ta farmaki kasar Cuba, a 1983 kuma ta kai mamaya a kasar Grenada wanda Majalisar Dinkin Duniya ta fito fili ta yi tir da hakan. Kazalika a 1989, ta kai hare-hare a Panama tare da tumbuke shugaban kasar Manuel Noriega bayan haddasa dimbin asarar rayukan fararen hula. Taho-taho har aka tsallako karni na 21, Amurka ba ta daina ta’asarta ba. Ta yi gaban kanta tare da wancakalar da dokokin kasa da kasa ta afka wa Iraqi a 2003, ta kuma zama kanwa-uwar-gamin wargaza kwanciyar hankalin Libiya a karkashin NATO a 2011. Wadannan duka wasu misalai ne kawai daga ta’asar da take tafkawa, baya ga yakin sunkuru na hana sakat a wasu kasashe.

Yanayin kasa da kasa ya riga ya shiga cikin wani mawuyacin hali da aka dade ba a ga irinsa ba sakamakon miyagun dabi’un Amurka, kuma galibi kamar yadda masharhanta da dama ke fada, ba don komai ba ne illa kare matsayinta na babakere a duniya. Harin da Amurka ta kai wa Venezuela ya kara tsananta fargabar al’umma a wasu yankuna da ake fama da rikice-rikice domin kar hakan ya zama silar murkushe kananan kasashen da ake rikici da su.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

A daya daga cikin jawabansa, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya taba bayyana cewa, bai kamata a mayar da duniyarmu ta karni 21 mai wayewar kai ta dan’adam ta koma rayuwa irin ta namun daji ba, watau babba ya rika farautar mai rauni.

Hakika, lokaci ya yi da za a amsa kiraye-kirayen kasar Sin na hada karfi da karfe wajen tabbatar da bin dokokin kasa da kasa a karkashin ikon Majalisar Dinkin Duniya. Harin da Amurka ta kai wa Venezuela ya wuce wani abu na yankin Latin da Caribbean kawai, gargadi ne da an kararwa game da halin da duniya ke ciki na cin zalin daga kasar da ke ganin babu mai nuna mata isa. Yana gaya wa duniya cewa har yanzu za a iya yin hakan a kwana lafiya, kuma bin dokokin kasa da kasa ba tilas ba ne zabi ne ga manyan kasashe.

Idan abin ya ci gaba a haka ba tare da an ja masa burki ba, tsarin duniya da ke cikin mawuyacin hali zai iya rugujewa, musamman ma ganin cewa, bayan Venezuela, yanzu haka Amurka ta maida hankali ga kwace yankin Greenland na kasar Denmark, lamarin da zai sake haifar da mummunan rudani a duniya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Venezuela
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Venezuela
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
An Kama Mutane 8 Da Ake Zargi Da Hannu A Harin Ƙunar Baƙin Wake A Masallacin Borno

An Kama Mutane 8 Da Ake Zargi Da Hannu A Harin Ƙunar Baƙin Wake A Masallacin Borno

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.