ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara: Gwamna Lawal Ya Jagoranci Taron Gaggawa Kan Tsaro

by Sulaiman
3 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jajanta wa al’ummomi da iyalan waɗanda hare-haren ’yan bindiga suka shafa a sassa daban-daban na jihar, yana mai tabbatar da ƙudurin gwamnatinsa na kawo ƙarshen matsalar tsaro da ta daɗe tana addabar yankin.

 

Gwamnan Lawal ya kira tare da jagorantar wani taron gaggawa na Majalisar Tsaron Jihar a ɗakin taro na Gidan Gwamnati da ke Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Kamfanonin Jamus Za Su Kara Zuba Jari Da Gudanar Da Kasuwancinsu A Kasar Sin
  • Dalilan Da Suke Sa Mata Samun Ƙarin Mahaifa (Fibroid) (2)

Taron ya haɗa shugabannin hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki domin duba halin da ake ciki da kuma ɗaukar matakan gaggawa.

 

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an bayyana cewa kiran taron ya biyo bayan rahotanni masu tayar da hankali, musamman sahihan bayanai kan zargin dasa bama-bamai na na’urorin fashewa (IED) a kan wasu manyan hanyoyin jihar.

 

Sanarwar ta ce, gwamnan ya umarci shugabannin hukumomin tsaro da su sake nazari kan tsarin tsaron da ake da shi a halin yanzu, tare da samar da ingantaccen tsari na aiki mai ma’ana, tsari da haɗin gwiwa domin daƙile wannan sabon salo na barazana.

 

“Taron ya nuna haɗin kai da ɗaukar alhakin bai ɗaya tsakanin gwamnatin jihar da hukumomin tsaro wajen kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Zamfara,” inji sanarwar.

 

Gwamna Lawal ya buƙaci hukumomin tsaro da su ƙara ƙaimi wajen tattara bayanan sirri, ƙara sanya ido da ɗaukar matakan haɗin gwiwa cikin gaggawa domin hana miyagun mutane ƙara samun galaba.

 

Ya jaddada muhimmancin kasancewa a gaba da masu aikata laifi, tare da taƙaita musu damar motsi da murƙushe duk wata barazana ba tare da jinkiri ba.

 

Bugu da ƙari, gwamnan ya miƙa saƙon ta’aziyya ga hukumomin tsaro bisa rasuwar jami’ansu da suka sadaukar da rayukansu wajen kare al’umma, tare da yi wa waɗanda suka jikkata fatan samun sauƙi cikin gaggawa.

 

Haka kuma, ya jajanta wa iyalan waɗanda suka rasa rayukansu da al’ummomin da hare-haren suka shafa, yana mai tabbatar da cewa gwamnati za ta ba da cikakken goyon baya na kayan aiki, dabaru da tsari domin ƙara ƙarfin hukumomin tsaro.

 

Gwamnatin Zamfara ta jaddada cewa za ta ci gaba da saukar dukkan matakan da suka dace domin dawo da zaman lafiya mai ɗorewa a faɗin jihar, tare da tabbatar da cewa tsaro ya zama ginshiƙin ci gaban al’umma.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

An Kashe Manjo Da ‘Yan Ta’adda 10 A Hare-haren Da Aka Daƙile Kan Sansanonin Soja

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.