ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hasashe Game Da Siyasar Nijeriya A 2027

by Sulaiman
5 months ago
vector illustration of Nigeria flag and map

vector illustration of Nigeria flag and map

Nan da shekara mai zuwa, wato 2027, Nijeriya za ta gudanar da zaɓe, wanda a tarihin kasar kamar ba a taɓa irinsa ba.

Jam’iyya mai mulki ta APC, ta shirya haɗiye duk fitattun ‘yan siyasa da suka yi shura da adawar APC, inda da yawa daga cikin masu rike da kujerun siyasa a jam’iyyoyin adawa ke rige-rigen sauya sheƙa zuwa APC.

Amma ko me hakan ke nufi, ko dai talala suke yi wa jam’iyyar daga karshe su gudu su barta?

ADVERTISEMENT

 

A ɓangare guda kuma, gamayyar wasu shugabannin siyasa masu adawa, sun haɗe a sabuwar jam’iyyar adawa ta ADC don tunkarar zabe mai zuwa, inda Kwankwaso kuma na Jam’iyyar NNPP ya jaddada cewa, yana da ƙwarin gwiwa zai lashe zaɓen dake tafe ba tare da ya sauya jam’iyya ba.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Bari mu yi dubawa kan wasu fitattun ‘yan siyasa a 2027.

 

Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso 

Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso fitaccen ɗan siyasa ne, wanda aka san shi da tasirinsa a siyasar Jihar Kano da kuma kafa ƙungiyar Kwankwasiyya da ke da ɗimbin matasa magoya bayan ɗan siyasar.

 

Kwankwaso ya shiga siyasa tun a jamhuriya ta Uku (1992–1999), inda aka zaɓe shi a matsayin Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano a 1992. Daga nan kuma, sojoji suka karɓi mulkin ƙasa wanda hakan ya dakatar da siyasarsa har sai da aka dawo mulkin farar hula (dimokuraɗiyya) a 1999.

 

Kwankwaso ya zama Gwamnan jihar Kano na farko a karkashin Jam’iyyar PDP bayan mulkin soji a shekarar 1999–2003. A lokacin mulkinsa, ya mai da hankali kan ilimi, kayayyakin more rayuwa, da ci gaban karkara, amma ya sha kaye a zaɓen da aka sake yi a 2003 sannan kuma ya sake lashe zaɓen Gwamna karo na biyu a 2011–2015.

 

Har ila yau, bayan ya cika wa’adin da kundin tsarin mulki ya tanadar masa na zama a kujerar Gwamna shekaru takwas kacal, Kwankwaso ya lashe zaɓen kujerar Sanata mai wakiltar Kano ta Tsakiya a 2015-2019.

 

An naɗa Kwankwaso a matsayin Ministan Tsaro (2003–2007) a ƙarƙashin Shugaba Olusegun Obasanjo bayan ya yi rashin nasara a hannun Malam Ibrahim Shekarau bayan zangonsa na farko kan kujerar Gwamnan Kano.

 

Asali babban jigo ne a PDP. Ya kuma zama babban mamba da suka kafa Jam’iyyar APC a 2013. Daga baya ya koma PDP, kuma a 2022, ya koma Jam’iyyar NNPP inda ya zama ɗan takarar shugaban ƙasa na NNPP a babban zaɓen 2023. Ya samu ruwan kuri’u, musamman a Jihar Kano.

 

A shirye-shiryen zaɓen 2027 da ke tafe, Kwankwaso yana ci gaba da tallata burinsa na siyasa, duk da cewa, babu wata sanarwa a hukumance, amma ana raɗe-raɗin yana taka rawar gani a cikin siyasar Nijeriya wanda ke sa shi watakila ya yi rashin tabbas a siyasar 2027.

 

Yayin da Atiku da Obi suka sauya sheka zuwa ADC, Kwankwaso ya ci gaba da zama jam’iyyar NNPP a matsayin tsani mai karfi, ya ki shiga kowace hadakar jam’iyyun adawa.

 

A makon jiya, a ranar 20 ga Disamba, 2025, ya shirya babban taron NNPP a Abuja, inda ya yi alfahari cewa NNPP ita ce jam’iyyar mafi daidaito da tsara a Nijeriya. Ya jaddada cewa burinsa na lashe zaben shugaban kasa a 2027, ba tare da zama dan takarar mataimakin shugaban kasa ga Atiku ko wani ba.

 

Bola Ahmed Tinubu

Bola Ahmed Tinubu fitaccen ɗan siyasa wanda aka fi sani da “ɗan fafutuka”, gina jam’iyya, sannan kuma yanzu, a matsayin shugaban ƙasa.

 

Ya fara siyasa a farkon shekarun 1990 a lokacin gwagwarmayar dimokuradiyya.

 

Ya zama babban jigo a cikin ƙungiyar masu fafutukar dimokuradiyya da ke adawa da mulkin soja bayan soke zaɓen 12 ga Yuni, 1993.

 

An zaɓi Tinubu a matsayin Sanata mai wakiltar Yammacin Legas a ƙarƙashin Jam’iyyar SDP a cikin ɗan gajeren lokaci na Jamhuriya ta Uku, inda aka katse jamhuriyar sakamakon ƙwace mulkin da sojoji suka yi a 1993.

 

Tinubu ya yi Gwamnan Jihar Legas a 1999–2007. Ya taka muhimmiyar rawa wajen kafa Jam’iyyar APC a 2013, wacce ta tattaro jam’iyyun adawa da dama.

 

Ya fafata a zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa na APC kuma ya yi nasara.

 

An zaɓe shi a matsayin shugaban Nijeriya a watan Fabrairun 2023, ya kama aiki a ranar 29 ga Mayu, 2023 har zuwa yau.

 

Bayan ya samu tikitin kai tsaye na jam’iyyarsa ta APC a fafatawar zaɓen 2027 don ya sake tsayawa takarar shugaban kasa karo na biyu, shekarar 2026 za ta kasance shekara mai matukar muhimmanci ga Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ganin cewa, itace jajibirin shekarar zaɓe. Lokacin mulkinsa na farko, an fuskanci kalubale na kunci da tsadar rayuwa biyo bayan cire tallafin man fetur da kuma kaddamar da wasu sauye-sauye a fanni tattalin arziki da nufin ɗaga darajar Naira.

 

Don haka, Mutane za su so ganin yadda zai sarrafa sakamakon wadannan manufofi masu tsauri ta hanyar yakin nema zabe. Zuwa farkon shekarar 2026, matsin tattalin arziki da ake fuskanta za su zama makamin siyasa mafi karfi a kasar nan. A al’ada, ‘yan Nijeriya suna kada kuri’asu ne bisa lura da asalin kabila da yanki, amma 2026 na iya nuna wani sauyi zuwa zaben da ake yin sa bisa kwazon gwamnati wajen samar da ababen more rayuwa.

 

…. za mu ci gaba a mako mai zuwa

Siyasa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.8 Cikin Dari A 2025

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.8 Cikin Dari A 2025

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.