Wani jami’in sojin Nijeriya da wasu dakaru shida sun rasu bayan ‘yan bindiga sun kai musu harin kwantan-ɓauna a ƙaramar hukumar Chikun ta Jihar Kaduna da yammacin ranar Litinin.
Majiyoyin tsaro sun ce sojojin suna kan sintiri ne yayin da suke dawowa daga wani aiki da suka yi nasara, lokacin da maharan suka farmake su.
An ce an gwabza ƙazamin faɗa tsakanin sojojin da maharan, inda duk da cewa sojojin sun mayar da martani tare da jikkata wasu daga cikin maharan, amma sojoji bakwai sun rasa rayukansu.
Harin ya faru ne duk da nasarorin da sojoji suka samu a ‘yan kwanakin nan a yankin Kaduna zuwa Zariya, inda suka lalata maɓoyar ‘yan bindiga, tare da ceto waɗanda aka yi garkuwa da su.
Hukumomin soja ba su fitar da cikakken bayani a hukumance ba, amma rahotanni sun ce an tura ƙarin dakarun soja zuwa yankin domin bin sahun maharan da kuma hana sake aukuwar irin wannan hari.














Discussion about this post