Ana ci gaba da aiwatar da shirin tallafin da Sin ta ware wa kasar Nepal, wanda ya hada da tallafin kudi na gaggawa da kuma taimakon jin kai, yayin da ake sa ran isar wasu kayayyakin agaji birnin Kathmandu nan ba da jimawa ba, kamar yadda ministan harkokin wajen Sin, Wang Yi, ya bayyana yayin tattaunawar da ya yi ta wayar tarho da takawaransa na kasar Nepal, Shisir Khanal a jiya Asabar.
Wang, wanda har ila yau mamba ne a ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin (JKS), ya ce mummunan ibtila’in zaftarewar kasa, wanda ya abku sakamakon ruftawar daskararriyar dusar kankara kwatsam a yankin kan iyakar Nepal, ya haifar da asarar rayuka masu yawa kuma ya haddasa bacewar mutane a bangarorin biyu.
Wannan shi ne ibtila’i mafi muni da ya abku a tsakanin kasashen biyu cikin ‘yan shekarun nan, kuma ayyukan ba da agaji a wurin sun kasance masu sarkakiya da wahala.Wang ya kara da cewa, a yayin da take hanzarta aiwatar da ayyukan ceto da ba da agaji a bangarenta, kasar Sin ta kuma tsara ba da taimako bisa damar da aka samu da wuri-wuri tare da tallafa wa Nepal a bangaren ayyukan ba da agajin gaggawa.
A cewar wani taron ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na Jam’iyyar Kwaminis ta Sin (JKS), kasar Sin za ta bayar da tallafin gaggawa ga yankin da ibtila’i ya abku a Nepal tare da gudanar da aikin ceto na hadin gwiwar kasa da kasa. Wannan, wani muhimmin mataki ne na siyasa da kasar Sin ta dauka, wanda ke nuna alakar abota tsakanin Sin da Nepal, kamar yadda ya bayyana.
An kai kayan agaji da kuma kwararrun ma’aikatan ceto hudu na kasar Sin ta hanyar jiragen dakon kaya kirar Y-20; inda suka isa filin jirgin sama na kasa da kasa na Tribhuvan da ke Kathmandu na kasar Nepal, da misalin karfe 7 na safe agogon kasar yau Lahadi, domin tallafa wa ayyukan ba da agajin gaggawa na ibtila’i.
Hukumar kula da rage hasara da gudanar da ayyukan ba da agajin ibtila’i ta kasar Nepal ta bayyana cewa, zuwa karfe 9 na safiyar yau Lahadi agogon kasar, an gano gawarwaki 734 daga yankunan da zaftarewar kasar ta abku, yayin da har yanzu ba a ji duriyar mutane 2,498 ba. (Abdulrazaq Yahuza Jere)














