ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Idan Kunne Ya Ji, Jiki Ya Tsira

by Sulaiman
1 year ago
Kunne

Hausawa na cewa, “idan kunne ya ji, jiki ya tsira.” Jama’a mu tambayi kanmu mana, wai me ke faruwa ne a kwanan nan tsakanin Amurka da ’yar goshin gabanta Ukraine? Amma kuma, za mu iya cewa, ba mamaki.

Shugaban Amurka, Donald Trump ya yi ikirarin cewa, a cikin sa’o’i 24 zai kawo karshen yakin Ukraine da Rasha wanda kasarsa ta kasance gaba-gaba wajen bayar da tallafin kudi da makamai ga kasar Ukraine. A kan wannan yunkuri ne, tawagar Amurka ta gana da takwararta ta Rasha a birnin Riyadh na Saudi Arabiya, inda suka tattauna batutuwa masu dadi. Duniya ta yi jim tana ta sake-saken yadda za ta kare da ’yar lele (Ukraine) a yayin tattaunawar da aka dade ana tsumayi tsakaninta da uwargidanta (Amurka).

  • Jami’an NDLEA Sun Kashe Budurwa A Kano, An Damƙe Su 
  • Sin Za Ta Kara Ingiza Samar Da Kudaden Gudanar Da Kamfanoni Masu Zaman Kansu

Ganawar da Trump ya yi da takwaransa na Ukraine Volodymyr Zelenskyy, a ofishin Oval ta bai wa duniya mamaki, inda aka tashi ba tare da cimma wata matsaya ba, wanda hakan ke barazana ga makomar Ukraine musamman inda shugaban ya yi biris da maganar kwantiragin ma’adanai na kasarsa ga Amurka.

ADVERTISEMENT

Wannan ziyarar ta bayyana wani hali na son kai na Amurka wanda ya fara dagula alakarta da kawayenta na yamma kunshe a matsayin “kariyar zaman lafiya” na gwamnatin Trump.

Don haka, shugabannin kasashen Turai suka gana a wani taro na gaggawa a birnin Paris a ranar Litinin domin mayar da martani kan sauyin manufofin Washington kan Kyiev, yayin da shugabar hukumar Tarayyar Turai Ursula von der Leyen ta ce, “Ana barazana ga tsaron Turai.”

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Har ila yau, jim kadan bayan ficewar Zelenskyy daga Washington, shugabannin kasashen Turai da suka hada da na Jamus da Faransa da Italiya da kuma Birtaniya suka yi gaggawar mara masa baya, yayin da wasu ‘yan majalisar dokokin Amurka suka yi kakkausar suka ga Ukraine wanda a cewar Sanata Lindsey Graham na jam’iyyar Republican ta South Carolina, “sanadiyyar wannan ganawar da ta bar baya da kura, ka iya kawo karshen goyon bayan Washington ga Kyiv.”

Shin abin tambaya a nan, da gaske ne wannan yunkurin na Amurka don kawo karshen rikici ne a tsakanin Ukraine da Rasha ko kuwa don amfanin kanta ne? Me ya sanya gwamnatin Trump ta fara wani gangamin tonon silili mai zafi kan Zelenskyy?

Kwanakin baya sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth ya yi nuni da cewa, yunkurin Ukraine na shiga kungiyar NATO abu ne mara tabbas, tare da bai wa Kyiv shawarar daina fatan mallakar wani yankin kasa daga Rasha. Washington ta tattauna da Moscow a Saudi Arabia ba tare da Kyiev ba, wanda hakan ke nuna cewa za a iya yanke shawarar makomar Ukraine ba tare da saninta ba.

Bugu da kari, Trump ya kira Zelenskyy a matsayin “mai mulkin kama karya,” yana zargin Kyiv da fara tsokano rikici da Moscow. Sannan ya bukaci Zelenskyy ya rattaba hannu kan yarjejeniyar ma’adinai da Amurka da sauri, in ba haka ba, zai iya rasa duka kasarsa ga Rasha. A yayin ganawarsu ta ranar Juma’a, Trump ya zargi Zelenskyy da yunkurin kawo yakin duniya na uku. Duk wannan barazanar don cimma muradan son zuciyar Amurka na matsawa Kyiev rattaba hannu kan yarjejeniyar ma’adanai.

Wannan a fili yake, Amurka tana son dawo da kudadenta na tallafin soji da ta bai wa Ukraine na tsawon shekaru ba don neman zaman lafiyar yankin ba.

Don haka, Trump ya ki la’akari da bukatar Zelenskyy na neman tabbatar masa da tsaro sai dai matsa masa kan amincewa da yarjejeniyar hakar ma’adanan Ukraine.

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Kunne
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Ziyarci Mambobin Majalisar CPPCC

Xi Jinping Ya Ziyarci Mambobin Majalisar CPPCC

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.