Shugaban rundunar ‘yansandan Nijeriya, IGP, Kayode Egbetokun, ya bukaci Jami’an hulda da jama’a na rundunar ‘yansanda a fadin kasar da su ƙara ƙaimi wajen yaƙi da labaran ƙarya, yana mai gargadin cewa, hakan na ƙara barazana ga amincin da rundunar ke da shi a idon jama’a.
Ya yi wannan kiran ne a taron jami’an hulda da jama’a na ‘yansanda na shekarar 2025.
- Bayan Tsare Jami’an Sojin Nijeriya A Burkina Faso, Nijar Ta Sanya Tsauraran Bincike Kan Kayayyakin Nijeriya
- Ƙalubalen Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Shi Da Alaƙa Da Addini — Gwamnatin Tarayya
Da yake jawabi a wurin taron, ya jaddada buƙatar hanzarta gano tsoffin bidiyo da ke sake bayyana a matsayin sabbi, ƙirƙirarrun hotuna, da ke bayyana a matsayin abubuwan da ke faruwa a yanzu.
Ya bukaci masu magana da yawun ‘yansandan da su rungumi dabarun tantance gaskiya da kuma mayar da martani cikin gaggawa ga labaran ƙarya kafin su yaɗu sosai.
Egbetokun ya kuma buƙaci jami’an da su mayar da kafofin sada zumunta zuwa wani dandali na tabbatar da gaskiya, bayyana gaskiya, da kuma tabbatar da amincin da jama’a ke da shi ga rundunar, yana mai jaddada cewa, yaɗa ingantattun labarai shi ne ginshiki ga aikin ‘yansanda na zamani.
ADVERTISEMENT














