ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Da Kishin Bunkasa Rayuwar Mata Da Kananan Yara Tun Ina Karama – Fatima Dala

by Abdullahi Muh'd Sheka
4 years ago
Mata

HAJIYA FATIMA ABDULLAHI DALA mashawarciya ta musamman ga Gwamnan Jihar Kano Kan harkokin Mata da kananan Yara, Shugabar Matan Jam’iyyar APC Ta Jihar Kano, guda cikin Masu rajin ganin Mata da kananan Yara sun amafana da tagomashin Gwamna Ganduje.

A tattaunawar ta da wakilinmu a Kano ABDULLAHI MUHAMMAD SHEKA, Fatima Dala ta bayyana Yadda ta taso cikin Gwagwarmaya musamman bangaren kishin ci gaban Mata, kananan Yara, Jagorancin Al’umma tun daga kasa. Ga dai yadda tattaunawar ta kasance:

  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Tsoho Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Har Abada Kan Laifin Fyade A Jigawa
  • 2023: Ana Rububin Kujerar Ahmed Lawan Bayan Soke Takararsa

Za muso ki gabatar wa da mai karatu kanki da kanki?

ADVERTISEMENT

Alhamdulillahi, ni dai kamar yadda aka sani sunana Hajiya Fatima Abdullahi Dala, haifaffiyar Jihar Kano a Karamar Hukumar Dala, na taso a Unguwar Dala, nafara Gwagwarmaya tun ina karamar, har kuma tsunduma harkokin siyasa wanda na zama mashawarciya ta musamman ga mai girma Gwamnan Kano a kan harkokin Mata da Kananan Yara sannan kuma a yanzu ni ce Shugabar matan Jam’iyyar APC ta Jihar Kano

Ya ya batun tarihin Gwagwarmayar Rayuwa?

LABARAI MASU NASABA

Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

Alhamdulillahi, ni kamar yadda aka sani mun taso cikin kyakkawar kulawar iyaye, wanda hakan yasa muka samu nutsuwa tare da neman yadda za mu taimaka wa Jama’a a dukkan matakin da muka samu kan mu a cikin, na fara Gwagwarmayar kungiyoyi tun daga cikin unguwa, har ta kai na tsundum a cikin harkokin siyasa, wadda na rike mukamin shugabancin mazaba, daga nan na taho karamar hukuma, kokari da Jajircewa ya sa Gwamna Ganduje nada ni mashawarciya ta musamman kan harkokin Mata da Kananan Yara har kuma zuwa yanzu da Allah ya damka shugabancin matan Jam’iyyar APC a hannuna.

Wadanne abubuwa ne suka tsaya miki a zuciya musammana matsayinki na mace kuma mai rike da madafun iko a cikin Jam’iyyar APC a Jihar Kano?

Wannan tambaya ta zama kamar fami a wuri na, amma alhamdulillahi buri na ya cika domin damar da Khadimul Islam Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya bani tun daga kan mukamin mashawarciya ta musamman a kan harkokin Mata da Kananan Yara har kuma yanzu da aka zabe ni a matsayin Shugabar matan Jam’iyyar APC ta Jihar Kano, na samu damar Kawo sauyi cikin abubuwan da suka addabi Mata da Kananan Yara, a nan dole na jinjina wa mai dakin Gwamna Farfesa Hafsat Abdullahi Ganduje bisa taimakawar da take wajen shigo da mata cikin harkokin gudanar da Gwamnati, wanda zuwa yanzu kafa fadin kasar nan babu Gwamnan da ya bai wa Mata irin Damar da Gwamna Ganduje ya bai wa Mata a Jihar Kano.

Mata

Shaye-shaye na cikin abubuwan da a baya Jihar Kano ta yi kauri suna a kan su, shin kowane kokari Gwamnati ta yi har aka shawo kan wannan matsala?

Ina tabbatar maka da cewa duk Nijeriya babu Gwamnan da ya shirya magance matsalar shaye-shaye kamar Gwamna Ganduje, domin da farko duk cikin Gwamnonin kasar nan shi ya fara samar da mashawarci na musamman kan matsalar shaye-shaye. Mai dakinsa Farfesa Hafsat Ganduje kuma ita ce Matar Gwamna daya tilo da ke Jagorantar kaddamar dakarun yaki da sha tare fataucin Miyagun Kwayoyi mata a fadin kananan Hukumomin Jihar Kano 44, Sannan shi ne Gwamna daya tilo da ya bada Umarnin cewa duk wani jami’in Gwamnatinsa Sai anyi masa gwaji an tabbatar ba shi da matsalar shaye-shaye.

Yanzu haka ‘yan watanni ya ragewa wannan gwamnati a kan karagar mulki, shin kwalliya ta biya kudin sabulu?

Madallah an zo wurin, ina tabbatar maka da cewa, ba maganar kudin sabulu ake a Kano ba, har kudin tutare ma ta biya, domin ayyukan da Gwamna Ganduje ya shimfida wa Kanawa sai an shafe sama da shekara hamsin ana amfanarsu, da farko dai dubi yadda Ganduje ya kawata birnin Kano da manyan gadojin sama da kasa wadanda kaf Nijeriya babu irin su, Kuma shi ne Gwamna daya tilo da bai taba batan watan biyan albashi ba, shi ne Gwamnan da ya kafa cibiyar koyar da sana’o’i irin na zamani wanda Babu irinta wadda aka sa a sunan attajirin Nan can asalin Jihar Kano Aliko Dagote da ma sauran ayyukan da babu su cikin alkawuran daya daukarwa Kanawa, misali karasa ayyukan da Gwamnatocin Baya sukayi watsi da su.

Me kike fatan Jama’a su dinga tuna ki da shi?

Kyakkawar tarbiyar da muka samu daga iyaye da Kuma ayyukan ci gaban Mata da Kananan Yara Wanda Gwamnatin Kano ta sauya rayuwarsu tare Inganta.

Me ki kafi sha’awa ta fuskar abinci?

Ai kasan bakanuwar asali ce ni, saboda mun ta’ammali da abinci Gargajiya wanda muka tashi da shi a al’adun abincin bahaushe, kamar daga tuwo, sinadaran alkama da sauransu.

Sutura fa wacce aka fi sha’awar sanyawa?

Farare da masu launin kore sannan Ina matukar farin dikin ganina cikin hijabi.

Mene sakonki na karshe?

Alhamdulillah, sakona shi ne fatan jama’a su sani ya ba kyauta tukuici, a kara himmatuwa wajen bai wa Gwamna da Gwamnatin Kano goyon baya tare da addu’ar dorewar zaman lafiya. Sannan kowa ya sani lokaci na kara matsowa na Zaben Shekara ta 2023, a yi kokarin karkade kuri’u domin Gwamna Ganduje ya tsayar da na’ibinsa Dakta Nasiru Yusif Gawuna a matsayin dan takarar da muke kyautatawa zaton gadon buzun Ganduje. Sannan muna godiya ga Malamai ma gada Annabawa bias gudunmawar addu’o’in da suke yi wawannan Gwamnati ba dare ba rana.

Mata
Abdullahi Muh'd Sheka
+ postsBio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran
Labarai

Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran

July 5, 2026
Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

July 5, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036
Labarai

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Next Post
Hadin Farfesun Kifi Na Zamani

Hadin Farfesun Kifi Na Zamani

LABARAI MASU NASABA

Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran

Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran

July 5, 2026
Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

July 5, 2026
LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 

LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 

July 5, 2026
Enekweci Ne Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya A Wasannin Commonwealth Na Bana

Enekweci Ne Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya A Wasannin Commonwealth Na Bana

July 5, 2026
Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.