Rundunar dakarun tsaron teku ta Sin ko CCG, na ci gaba da sintirin wanzar da doka a sassan yankunan ruwa na gabashin tsibirin Taiwan, kamar yadda kakakinta ya bayyana a Asabar din nan. Mai magana da yawun rundunar Jiang Lue, ya ce jami’anta masu aiki a jirgin ruwa na Xiushan, sun karbi aiki daga takwarorinsu na jirgin ruwan Daishan a yau din, don ci gaba da gudanar da sintirin tabbatar da oda, bisa tanadin doka a sassan ruwan yankin gabashin tsibirin Taiwan.
Jiang ya kara da cewa tun daga watan Yuni, dakarun masu aiki karkashin rukunin jirgin ruwan Daishan sun gudanar da sintiri da ayyukan sanya ido, tare da samar da kariya ga masunta, da ayyukan ceto a yankunan ruwa masu nasaba, kana sun tabbatar da gudanar sufurin ruwa yadda ya kamata, da ayyukan kamun kifi, da halastattun hakkoki da moriyar jama’a, da kare rayuka da dukiyoyi na masunta Sinawa, ciki har da na ‘yan uwa mutanen Taiwan.
Bugu da kari, a cewar kakakin na CCG, rundunar za ta ci gaba da karfafa sintirin kare doka a yankunan ruwa dake karkashin ikon kasar Sin, da kare hurumin yankunanta, da hakkoki da moriyar kasa na yankunan ruwanta. (Saminu Alhassan)













