Shahararren ɗan wasan ƙwallon kwando a Duniya kuma wanda ke riƙe da tarihin wanda ya fi kowa jefa ƙwallaye a babbar gasar ƙwallon kwando ta NBA LeBron James, zai bar ƙungiyar Los Angeles Lakers ta ƙasar Amurka zuwa wata ƙungiyar dake buga gasar NBA.
A cewar rahotannin kafofin watsa labarai, ɗan wasan gaban mai shekaru 41 ya sanar da ƙungiyar Los Angeles cewa shekaru takwas da ya yi tare da Lakers ɗin sun zo ƙarshe, amma kuma zai buga kakar wasa ta 24 a gasar tare da wata ƙungiya ta daban, kamar yadda wakilin zakaran na NBA Rich Paul ya shaida wa ESPN.
Kwantiragin “King James,” wanda ya lashe gasar NBA tare da Lakers a shekarar 2020, ya ƙare bayan fitar da Lakers daga gasar a zagaye na biyu, “James ya zaɓi ya sanar da Lakers ƙudurinsa tun kafin fara gasar saboda ladabi da godiya akan tsawon lokacin da suka shafe” in ji Shams Charania na ESPN, rahoton shi ne tabbaci na farko cewa James zai ci gaba da buga gasar wadda ya lashe sau huɗu a tarihi tare da manyan nasarori da babu wani ɗan wasan kwando da ya taɓa samu, ana danganta James da yiwuwar komawa Cleɓeland ko Miami, ƙungiyoyi biyu da a a baya ya jagoranta wajen lashe kofuna, ko kuma ya iske abokinsa na ƙud da ƙud Stephen Curry a Golden State Warriors.














