Ministan tsaron Iran na riƙo ya ce ƙasar ba ta yarda da maƙiyanta ba, kuma zaune ƙasar take a shirye wajen fuskantar duk wani hari, yana gargaɗin cewa idan aka karya yarjejeniyar tsagaita wuta za su mayar da martani cikin gaggawa da ƙarfi.
A cewarsa, Iran a shirye take ta kare kanta a kowane lokaci, inda ya jaddada cewa rundunar ƙasar na cikin cikakken shirin tunkarar duk wani hari daga waje.
Wannan jawabi ya zo ne yayin wata tattaunawa ta wayar tarho da mataimakin firaministan Ƙatar kuma ministan tsaro, inda ɓangarorin biyu suka tattauna batutuwan tsaro da kuma yiwuwar ƙara haɗin gwiwar tsaro tsakaninsu.
Ministan ya kuma nuna damuwa kan yadda wasu ƙasashen waje ke shiga harkokin yankin, yana mai cewa hakan ba ya samar da tsaro sai dai yana ƙara rikici da rashin amincewa tsakanin ƙasashe, yana mai kira da a bar ƙasashen yankin su kula da tsaronsu da kansu.
Wannan dai na zuwa ne yayin da rikici ya ƙaru tun bayan hare‑haren Amurka da Isra’ila a ranar 28 ga Fabrairu, wanda ya sa Iran ta mayar da martani har da kai farmaki kan wasu wurare a Ƙatar.
A yanzu haka, Ƙatar tare da Pakistan na ƙoƙarin shiga tsakani domin samar da yarjejeniyar zaman lafiya ta dindindin tsakanin Iran da Amurka.
Ba mu tsara wata tattaunawa da Amurka ba a Doha
Iran ta musanta iƙirarin Trump cewa za a fara sabbin tattaunawa da Amurka a Doha, tana mai cewa ba ta tsara wata ganawa ko tattaunawa da Amurka ba a wannan lokaci ba.
Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta ce wakilan ƙasar da ke tafiya Doha ba don tattaunawa ba ne, sai dai domin bibiyar batun kuɗaɗen ƙasar da aka ƙwace a ƙasashen waje.
Wannan matsaya na Tehran ya zo ne duk da cewa Trump ya bayyana cewa za a gudanar da ganawa tsakanin wakilan ƙasashen biyu a babban birnin Ƙatar.
Sai dai jami’an Iran sun musanta wannan batu, suna jaddada cewa babu wani shiri na ganawa ko tattaunawa da suka shirya yi da Amurka a kwanaki masu zuwa.
A wani ɓangare, Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya ce kimanin dala biliyan 6 daga cikin biliyan 12 na kuɗaɗen Iran da aka ƙwace za su sake dawowa da su hannun gwamnati nan ba da jimawa ba.
Ya ce ana ci gaba da bin matakan da suka dace domin ganin an saki kuɗaɗen, wanda ake ganin zai taimaka wajen ƙarfafa tattalin arzikin ƙasar.
Haka kuma, Iran ta yi martani ga bayanan da shugaban Faransa Emmanuel Macron ya yi, inda ta jaddada cewa ita kaɗai ce ke da ikon gudanar harkokin mashigin Hormuz.













