ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Enekweci Ne Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya A Wasannin Commonwealth Na Bana

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago

Hukumar wasanni ta ƙasa (NSC) ta naɗa fitaccen ɗan wasan Nijeriya, Chukwuebuka Enekwechi, a matsayin kyaftin na tawagar Nijeriya a wasannin Commonwealth na wannan shekarar ta 2026 a birnin Glasgow na ƙasar Scotland, saboda girmama nasarorin da ya samu da kuma kyakkyawan wakilcin da ya yi wa Nijeriya a wasannin ƙasa da ƙasa, an sanar da naɗin ne a cikin wata sanarwa da Kola Daniel, mataimaki na musamman kan kafafen yaɗa labarai ga Darakta Janar na NSC, ya sanya wa hannu kuma aka raba wa manema labarai a ranar Talata.

Enekwechi zai jagoranci tawagar Nijeriya tare da Folashade Oluwafemiayo, wacce ta lashe kyautar zinare sau biyu a gasar Paralympic, wacce za ta kasance kyaftin a ɓangaren mata a wasannin da za’a fara a ranar 23 ga watan Yuli, ɗan wasan mai shekaru 33 da ke zaune a ƙasar Amurka ya kasance ɗaya daga cikin fitattun yan wasa daga nahiyar Afirika da za su fafata a gasar, shi ne zakaran da ya lashe kyautar gwarzon Afirka, ya lashe zinare a gasar wasannin Afirka ta 2019, ya kuma lashe kyautar azurfa a gasar Commonwealth ta shekarar 2018, inda ya zama ɗaya daga cikin yan wasa mafi nasara daga wannan ɓangaren a Nijeriya.

Darakta Janar na hukumar wasanni ta ƙasa (NSC), Hon. Bukola Olopade, ya ce naɗin ya nuna jajircewar hukumar wajen kyautatawa waɗanda suka bayar da gudunmawarsu wajen samun kyaututtuka a wasannin ƙasa da ƙasa ta hanyar bayar da jagoranci ga waɗanda suka cancanta, a cewar Olopade, dukkan kyaftin ɗin na wannan karon sun nuna ɗabi’un ladabi, juriya, kishin ƙasa da mutuntawa, inda halayyarsu ya zama abin koyi ga matasan yan wasa.

ADVERTISEMENT

“Mun zaɓi mutane waɗanda ba kawai tarihi mai kyau garesu a wasanninsu ba, sun nuna alama na iya jagoranci kuma sun yi aiki a matsayin masu ba da shawara ga matasan yan wasa ta hanyar ƙwarewa, jajircewarsu da kuma sadaukarwarsu ga Nijeriya,” in ji Olopade, ya ƙara da cewa naɗin ya kuma zama girmamawa ga sadaukarwar da ƴan wasan biyu suka yi wajen wakiltar ƙasar a wasannin ƙasa da ƙasa.

“Shawarar da muka yanke na ba su jagorancin tawagar Nijeriya ita ce kuma hanyarmu ta yaba wa ga gudummawar da suka bayar wajen ɗaga martabar Nijeriya a wasannin Duniya, NSC ta yi imanin cewa ƙwararrun ƴan wasan biyu za su taka muhimmiyar rawa a jagoranci a ciki da wajen filin wasa, inda za su taimaka wa matasan yan wasa su jure matsin lamba na shiga ɗaya daga cikin manyan wasannin Commonwealth.

LABARAI MASU NASABA

Yadda ‘Yan Spain Suka Mamaye Kyaututtukan Kofin Duniya

Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?

An shirya cewa tawagar Nijeriya za ta bar ƙasar a ranar 2 ga watan Yuli domin yin atisayen makonni uku kafin wasannin a birnin Aberdeen, inda ƴan wasan za su kammala shirye-shiryensu na ƙarshe kafin su tafi Glasgow, hakazalika tawagar ta bayyana cewar ta ƙulla yarjejeniya da kamfanin PUMA wajen samarwa yan wasan tufafin wasa, za a gabatar da kayan wasan ga tawagar a ranar 1 ga watan Yuli.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe
  • Abubakar Sulaiman
    Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu
  • Abubakar Sulaiman
    Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

MASU ALAKA

Yadda ‘Yan Spain Suka Mamaye Kyaututtukan Kofin Duniya
Wasanni

Yadda ‘Yan Spain Suka Mamaye Kyaututtukan Kofin Duniya

July 24, 2026
Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?
Wasanni

Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?

July 24, 2026
Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032
Wasanni

Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032

July 23, 2026
Next Post
LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 

LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

July 25, 2026

Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

July 25, 2026
Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

July 25, 2026
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026

Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu

July 25, 2026
Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

July 25, 2026

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026
Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

July 25, 2026
An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.