Hukumar wasanni ta ƙasa (NSC) ta naɗa fitaccen ɗan wasan Nijeriya, Chukwuebuka Enekwechi, a matsayin kyaftin na tawagar Nijeriya a wasannin Commonwealth na wannan shekarar ta 2026 a birnin Glasgow na ƙasar Scotland, saboda girmama nasarorin da ya samu da kuma kyakkyawan wakilcin da ya yi wa Nijeriya a wasannin ƙasa da ƙasa, an sanar da naɗin ne a cikin wata sanarwa da Kola Daniel, mataimaki na musamman kan kafafen yaɗa labarai ga Darakta Janar na NSC, ya sanya wa hannu kuma aka raba wa manema labarai a ranar Talata.
Enekwechi zai jagoranci tawagar Nijeriya tare da Folashade Oluwafemiayo, wacce ta lashe kyautar zinare sau biyu a gasar Paralympic, wacce za ta kasance kyaftin a ɓangaren mata a wasannin da za’a fara a ranar 23 ga watan Yuli, ɗan wasan mai shekaru 33 da ke zaune a ƙasar Amurka ya kasance ɗaya daga cikin fitattun yan wasa daga nahiyar Afirika da za su fafata a gasar, shi ne zakaran da ya lashe kyautar gwarzon Afirka, ya lashe zinare a gasar wasannin Afirka ta 2019, ya kuma lashe kyautar azurfa a gasar Commonwealth ta shekarar 2018, inda ya zama ɗaya daga cikin yan wasa mafi nasara daga wannan ɓangaren a Nijeriya.
Darakta Janar na hukumar wasanni ta ƙasa (NSC), Hon. Bukola Olopade, ya ce naɗin ya nuna jajircewar hukumar wajen kyautatawa waɗanda suka bayar da gudunmawarsu wajen samun kyaututtuka a wasannin ƙasa da ƙasa ta hanyar bayar da jagoranci ga waɗanda suka cancanta, a cewar Olopade, dukkan kyaftin ɗin na wannan karon sun nuna ɗabi’un ladabi, juriya, kishin ƙasa da mutuntawa, inda halayyarsu ya zama abin koyi ga matasan yan wasa.
“Mun zaɓi mutane waɗanda ba kawai tarihi mai kyau garesu a wasanninsu ba, sun nuna alama na iya jagoranci kuma sun yi aiki a matsayin masu ba da shawara ga matasan yan wasa ta hanyar ƙwarewa, jajircewarsu da kuma sadaukarwarsu ga Nijeriya,” in ji Olopade, ya ƙara da cewa naɗin ya kuma zama girmamawa ga sadaukarwar da ƴan wasan biyu suka yi wajen wakiltar ƙasar a wasannin ƙasa da ƙasa.
“Shawarar da muka yanke na ba su jagorancin tawagar Nijeriya ita ce kuma hanyarmu ta yaba wa ga gudummawar da suka bayar wajen ɗaga martabar Nijeriya a wasannin Duniya, NSC ta yi imanin cewa ƙwararrun ƴan wasan biyu za su taka muhimmiyar rawa a jagoranci a ciki da wajen filin wasa, inda za su taimaka wa matasan yan wasa su jure matsin lamba na shiga ɗaya daga cikin manyan wasannin Commonwealth.
An shirya cewa tawagar Nijeriya za ta bar ƙasar a ranar 2 ga watan Yuli domin yin atisayen makonni uku kafin wasannin a birnin Aberdeen, inda ƴan wasan za su kammala shirye-shiryensu na ƙarshe kafin su tafi Glasgow, hakazalika tawagar ta bayyana cewar ta ƙulla yarjejeniya da kamfanin PUMA wajen samarwa yan wasan tufafin wasa, za a gabatar da kayan wasan ga tawagar a ranar 1 ga watan Yuli.













