An yi bikin baje kolin tsarin samar da kayayyaki na duniya na Sin karo na 4, wato CISCE a takaice, a birnin Beijing daga ranar 22 zuwa 26 ga watan Yunin shekarar nan ta 2026, inda mataimakin shugaban kasar Afirka ta Kudu Paul Mashatile ya halarci bikin.
Wannan ne karo na biyu da Paul Mashatile ya halarci wannan biki, bayan wanda ya halarta a bara.Yayin da yake zantawa da wakilin babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG, Paul Mashatile ya ce, CISCE na da matukar muhimmanci ga kasarsa, saboda Sin aminiyar cinikayya ce mafi girma ga Afirka ta Kudu, kuma a ganin Afirka ta Kudu, ya dace a rika nuna kayayyakin musamman na kasar, gami da kwarewarta a fannoni daban-daban, da kokarin neman damarmakin hadin gwiwa karkashin dandalin na CISCE.
Sau da dama, mista Paul Mashatile ya sha ziyartar kasar Sin, ya kuma bayyana mamaki game da saurin ci gaban kasar da ya shaida, yana mai cewa, ya kamata a dubi abubuwan da kasar Sin ta aiwatar, a yi koyi da yadda take tsara shirye-shiryenta, gami da aiwatar da su a zahirance.
Mashatile, ya kuma yaba wa kasar Sin bisa matakinta na soke dukkanin haraji a kan kayayyakin kasashen Afirka 53 da suka kulla huldar jakadanci da ita, inda ya bayyana manufar da abu mai matukar kyau, wadda kuma Afirka ta Kudu ta yi maraba da ita.
Kazalika, Mashatile ya musanta zargin da ake yi wa hadin gwiwar Sin da Afirka, inda ya jaddada cewa: “Abun da muke gani shi ne sakamako mai gamsarwa, kuma ba mu taba ganin sakamako marar kyau, kamar yadda suke siffantawa ba.” (Murtala Zhang)













