Jama’a barkanmu da shigowa wata mai alfarma watan Ramadan, barkanmu da sake kasancewa tare da wannan shafi na GORON JUMA’A. Shafi ne da yake bawa kowa damar mika sakon gaishe-gaishensa, zuwa ga ‘yan’uwa da abokan arziki, na kusa da na nesa, har ma da wadanda aka dade ba a hadu ba. Kamar kowane mako, yau ma shafin na tafe da wasu sakonnin gaishe-gaishen naku da kuka aiko mana kamar haka; Da farko ina mika gaisuwa ga Babban Editanmu Alhaji Bello Hamza da fatan yana cikin koshin lafiya.
ako daga Alaja Habibah Idris Jihar Sokoto:
Ina gaida Mahaifana Alhaji Idris Mai Kabewa, da Hajiya Lantana mai Goro, ina gaishe da ‘yan uwana maza da mata na gida dana waje. Ina gaida kawayena Zuby Hamza, Samira Yakub, Amina Garba, Taisir Ahmad, da fatan sun sha ruwa lafiya, sannan da fatan sun yi sallar juma’a lafiya
Sako daga Awwal Amin Jihar Katsina:
Ina gaida Masoyiyata Fatima Yusuf Liman, ina gaida kannenta da yayyenta da mummynta gabadaya har da kawayenta, ni ne masoyinta mai kaunarta, har abada in sha Allah. Ina gaida abokaina Musa shanawa, Aminu Ak, Ibrahim mai hula da sauran ‘yan uwa na gida, Allah ya sa sun yi juma’a lafiya Allah ya bamu ladan Ibada.
Sako daga Abba Cele Jihar Kaduna:
Ina gaishe da Bilkisu Billy, ina gaishe da yayana Alhaji Hamisu mai walda Allah ya sa ka gama lafiya. Ina gaishe da babban abokina kuma amini na Salis Yusif, ina gaishe da abokaina na ko ina, da fatan za su yi juma’a lafiya.
Sako daga Hajiya Asma’u Lawan Jihar Kaduna:
Ina mika sako na zuwa ga ‘ya’yana Amina, da Hauwa, da Binta, da Zubaida, da Mu’allim, da Hassan da Hussaini da babban yayansu. Ina gaishe da masu adashi, ina gaishe da kawata Hajiya Murjanatu Ta Saraki, da yayyana, da sauran abokan arziki, Allah ya maimaita mana juma’a amin, a sha ruwa lafiya.
Sako daga Zeenat Idris Jihar Bauchi:
Ina mika sakon Goron Juma’a ga dukkanin iyalanmu baki daya, ina gaishe da al’ummar musulmin duniya, kawayena da saura ‘yan school dinmu, kannena da yayyena baki daya, da fatan sun sha ruwa lafiya, kuma da fatan kowa zai yi kwalliyar juma’a tare da yin sallar juma’a lafiya.
Sako daga Aina’u Ibrahim Jihar Kaduna:
ina gaishe da Khaleed, Nauwara, Habibah, zulaihat, sajida da fatan za su yi juma’a lafiya, sannan kuma sakon barka da shan ruwa zuwa ga ‘yan gidanmu da fatan kowa zai sha ruwa lafiya.
Sakon daga Sa’id Ahmad Sa’id Jihar Katsina:
Ina gaida abokaina ina gaida mahaifana da ‘yan Club dinmu, ina gaida Aisha da Husnah, ina gaida Mujahid da Anwar da Saleem da fatan za su yi sallar Juma’a lafiya.
Sako daga Hajiya Talatu Munjibir:
Ina yi wa duk al’ummar musulmi na fadin duniya barka da juma’a, kuma ina yi wa iyalaina barka da juma’a, da fatan kowa zai yi juma’a lafiya.
Sako daga Mamuda Al’amin Jihar Kaduna:
Ina gaida Yayata Fatima, kannen Farida, iyayena , ina yi wa kowa barka da juma’a.















Discussion about this post