ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Injiniya Murtala Ibrahim Sheme Ya Ɗauki Nauyin Jinyar Mutum 200 A Faskari

by Awwal Jibril Ƴan Kara
3 weeks ago
ibrahim

An gudanar da ayyukan tiyata kyauta ga maza da mata har mutum 200 daga garuruwa daban-daban na Ƙaramar Hukumar Faskari da ke Jihar Katsina a asibitin Shema, inda Injiniya Murtala Ibrahim Sheme ya ɗauki nauyin gudanar da ayyukan da waɗanda ke fama da matsalolin lafiya daban-daban.

Aikin tiyatar ya haɗa da cire gwaiwa da gyaran hainiya (hernia) da sauran matsalolin lafiya da ke buƙatar kulawar tiyata. Wannan taimako ya kasance wata babbar dama ga marasa lafiya, musamman waɗanda ba su da halin ɗaukar nauyin kuɗin jinya da tiyata da kansu.

Wannan gagarumin tallafi bai tsaya ga wani gari guda ba, maza da mata daga garuruwa daban-daban na faɗin Ƙaramar Hukumar Faskaria Jihar Katsina, ne suka samu damar amfana da wannan tallafi.

ADVERTISEMENT

Daga cikin waɗanda suka samu tallafin sun haɗa da Abdulsamad Umar daga Faskari da Abubakar Bishor daga Faskari da Yahaya Musa daga Daudawa da Magaji Audu daga Maigora da Sa’ade Ibrahim daga Maigora da Bahari Musa daga Dan Murai da Haruna Yakubu daga Ruwan Godiya da Hadiza Balarabe daga Yankara da dai sauran bayin Allah da suka samu damar cin gajiyar wannan taimako.

Wannan tallafi ya zo ne a wani muhimmin lokaci, inda wasu daga cikinsu ke buƙatar tiyata amma ba su da ikon ɗaukar nauyin kuɗin jinya da kansu.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ɗaukar nauyin irin wannan aiki na kiwon lafiya na daga cikin ayyukan da ke da matuƙar tasiri a rayuwar al’umma. Domin a lokuta da dama, kuɗin tiyata da sauran kuɗaɗen jinya kan zama babban ƙalubale ga marasa ƙarfi.

Ta hanyar wannan tallafin, an bai wa mutane masu yawa damar samun kulawar da suke buƙata ba tare da fuskantar nauyin kuɗin tiyata su ba.

Injiniya Murtala ya nuna cewa taimakon al’umma bai kamata ya tsaya ga magana kawai ba, ya kamata ya kasance aiki, sadaukarwa da ƙoƙarin inganta rayuwar jama’a.

Wasu daga cikin mutanen da suka samu aikin tiyatar, da kuma jama’ar da suka shaida wannan taimako, sun bayyana godiyarsu tare da addu’ar Allah ya saka wa Injiniya Murtala da alheri.

Haka kuma, wasu daga cikin waɗanda ba su samu damar shiga wannan karon ba, na ci gaba da fatan samun irin wannan dama a nan gaba. 

Aikin tiyatar ya gudana ne ƙarƙashin kulawar Ismail Yusif Sheme (AS) da Ahmad Iliya Sheme da Abubakar Musa, tare da sauran waɗanda suka ba da gudunmawa wajen ganin an gudanar da aikin cikin tsari.

ibrahim
Awwal Jibril Ƴan Kara
+ postsBio
    This author does not have any more posts.

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
ibrahim

Rushewar Gidaje Biyu Ta Yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 5 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.