Aƙalla mutane biyar ne suka rasa rayukansu bayan rushewar gine-gine biyu a Jihar Kano a ranar Asabar, 15 ga Agusta, 2026. Hukumar kashe gobara ta jihar ta ce lamarin ya faru ne a yankin Gaida da ke Ƙaramar Hukumar Kumbotso da kuma Kurna da ke Karamar Hukumar Fagge.
Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, ACFO Saminu Yusif Abdullahi, ya ce an samu kiran neman agajin gaggawa kan lamarin da misalin ƙarfe 2:34 na rana a Gaida, sannan aka sake samun wani kiran da misalin 2:40 na rana kan rushewar ginin da ke Kurna. A Gaida, wani ginin da ake ginawa da ke kusa da gidan nan Salbas da ya rushe yayin da ma’aikata shida ke aiki a wurin.
Ma’aikatan biyu, Muhammad Hassan mai shekaru 17 da Khalid Abubakar mai shekaru 19, sun tsira da ransu. Sai dai wasu hudu, Sunusi Surajo mai shekaru 18, da Bashir Ibrahim mai shekaru 20, da Ibrahim Ibrahim mai shekaru 25 da Abubakar mai shekaru 30, an ciro su a sume kafin daga bisani aka tabbatar da rasuwarsu. An kai gawarwakinsu Asibitin Murtala Muhammad kafin a miƙa su ga ƴansanda.
A wani lamari na daban, wani ginin makarantar Islamiyya ta Khadija Idris Bala da ke Kurna, bayan wata makarantar firamare a Ƙaramar Hukumar Fagge, ya rushe tare da rutsa ɗalibai tara a ciki. Ɗalibai takwas masu shekaru tsakanin 12 zuwa 15 sun tsira, yayin da Khadija Muhammad mai shekaru 14 aka ciro ta a sume, amma daga bisani ta rasu.
Hukumar kashe gobara ta ce har yanzu ba a gano musabbabin rushewar gine-ginen biyu ba, yayin da ake ci gaba da bincike. Hukumar ta kuma buƙaci masu gine-gine, da ƴan kwangila da ma’aikata su kiyaye ƙa’idojin gini da matakan tsaro, musamman a lokacin damina, domin rage haɗarin sake faruwar irin waɗannan iftila’in.














