Masu sa ido kan harkokin tsaron teku da ke Birtaniya sun tabbatar da cewa wasu jiragen ruwa na kasuwanci guda uku sun bayar da rahoton kai musu hare-hare daga wasu ƙananan jiragen yaƙi a mashigin ruwa na Hormuz, wanda ke da matuƙar muhimmanci kuma inda dakarun Amurka da na Iran ke fafatawa domin iko da yankin.
Dakarun juyin juya halin Iran, IRGC, sun bayyana a ranar Laraba cewa rundunar ruwansu ta kwace wasu jiragen dakon kaya guda biyu da suka yi ƙoƙarin ketare Mashigin Hormuz, duk da cewa Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sanar da tsawaita tsagaita wuta domin ba da ƙarin lokaci ga tattaunawa.
Duk da sabbin hare-haren da ake kai wa zirga-zirgar jiragen ruwa a yankin Gulf, rahotanni sun nuna cewa za a iya gudanar da zagaye na biyu na tattaunawar Amurka da Iran cikin kwanaki biyu zuwa uku masu zuwa, kamar yadda ‘New York Post’ ta rawaito.
A cikin wata sanarwa, IRGC ta ce: “Rundunar ruwan IRGC ta gano tare da tsayar da wasu jiragen ruwa biyu masu karya doka a safiyar yau a Mashigin Hormuz.”Sanarwar ta ƙara da cewa: “An kwace jiragen ruwan biyu da suka karya doka… kuma rundunar ruwan IRGC ta mayar da su zuwa gabar tekun Iran.”















Discussion about this post