ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankin Duniya Zai Bai Wa Nijeriya Rancen Dala Biliyan 1.25 Duk Da Ƙorafin Da ‘Yan Ƙasar Suka Yi

by Sadiq
3 weeks ago

Bankin Duniya ya amince zai bai wa Nijeriya sabon rancen dala biliyan 1.25 a ƙarƙashin shirin NAIJA domin tallafawa wajen zuba jari da samar da ayyukan yi.

An sanar da amincewar ne tare da ƙaddamar da sabon tsarin haɗin gwiwa tsakanin Bankin Duniya da Nijeriya na shekarun 2026 zuwa 2032.

Bankin ya ce kuɗin za su taimaka wajen samar da ayyukan yi, bunƙasa kasuwanci, inganta wutar lantarki, faɗaɗa intanet, inganta harkokin lafiya da kuma haɓaka noma.

ADVERTISEMENT

Daraktan Bankin Duniya a Nujeriya, Mathew Verghis, ya ce manufar shirin ita ce tabbatar da cewa sauye-sauyen tattalin arziƙin da aka fara sun samar da ci gaba a rayuwar ‘yan Nijeriya ta hanyar jawo masu zuba jari da samar da ƙarin ayyukan yi.

Bankin ya ƙara da cewa kuɗin za su kuma tallafa wajen gyare-gyare a fannin wutar lantarki, tattalin arziƙin zamani, noma, kasuwanci da kuma ƙara samar da kuɗaɗen shiga na gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Sai dai wannan mataki ya haifar da ce-ce-ku-ce kan ƙaruwar basussukan da Nijeriya ke karɓowa.

Wasu ‘yan Nijeriya na ganin gwamnati na ci gaba da karɓar rance daga ƙasashen waje duk da matsin tattalin arziƙin da al’umma ke fuskanta.

Alƙaluman Hukumar Kula da Basussuka ta Ƙasa (DMO), ta fitar ya nuna cewar bashin da Bankin Duniya yake bin Nijeriya ya ƙaru daga dala biliyan 17.81 a ƙarshen shekarar 2024 zuwa dala biliyan 19.89 a ƙarshen shekarar 2025, lamarin da ya sa Bankin Duniya ya kasance mafi girman wanda yake bai wa Nijeriya rance a cikin cibiyoyin kuɗi na duniya.

MASU ALAKA

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya
Manyan Labarai

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

July 24, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 24, 2026
Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC
Manyan Labarai

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

July 23, 2026
Next Post
An Kama Tsohon Minista Uche Nnaji Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi

An Kama Tsohon Minista Uche Nnaji Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi

LABARAI MASU NASABA

NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

July 24, 2026
Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

July 24, 2026
Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.