Iyalan Alƙalin Babbar Kotun Jihar Kebbi, Mai Shari’a Faruk Hassan Bunza, wanda aka yi garkuwa da shi daga gidansa, sun tabbatar da cewa sun biya Naira miliyan 50 a matsayin kuɗin fansa domin a sako shi.
An yi garkuwa da Mai Shari’a Bunza ne da sanyin safiyar ranar Lahadi, 26 ga Yuli, lokacin da wasu ‘yan bindiga ɗauke da muggan makamai suka mamaye gidansa da ke Ƙaramar Hukumar Bunza a Jihar Kebbi.
Alƙalin ya samu ‘yancinsa ne a ranar Litinin bayan shafe kwanaki takwas a hannun masu garkuwa da mutanen.
Wani ɗan uwansa, wanda ya yi magana da Daily Trust bisa sharadin kada a bayyana sunansa saboda ba shi da izinin yin bayani kan lamarin, ya tabbatar da cewa an biya Naira miliyan 50 ga masu garkuwa da mutanen.
Ya ce alƙalin na samun kulawa a gidansa da ke Bunza kuma yana ci gaba da murmurewa.
A cewar majiyar, da farko masu garkuwar sun nemi Naira miliyan 200 a matsayin kuɗin fansa, amma bayan kwanaki ana tattaunawa da su, sun amince da karɓar Naira miliyan 50 kafin su sako alƙalin.












