ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iyaye Mu Kara Himmar Samar Da Al’umma Mai Tarin Ilimi –Matar Gwamnan Katsina

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
Matar Gwamnan katsina

An gudanar da gasar adabi domin bunkasa ilimin ‘ya ‘ya mata karo na uku mai taken ‘Fatima Dikko Radda girls child education summit and literacy contest’.

Ita dai wannan gasa na da nufin karfafa gwiwar ‘ya ‘ya mata musamman abinda ya shafi karatun su tun daga matakin firamare har zuwa jami’a ta yadda za su rika samun wakilci a duk sauran al’amura.

  • Gwamna Radda Ya Yi Allah Wadai Da Hare-haren ‘Yan Fashin Daji A Jihar Katsina 
  • Yadda Mahara Suka Kashe Mutane Da Sace Wasu Da Dama A Wurin Maulidi A Katsina

A karo na uku na wannan gasa, an zakulo dalibai daga bangarori hudu da suka hada da karamar sikadara da babar sikadare da masu digiri da kuma masu digiri na biyu domin fafatawa a wannan gasa wanda kungiyar ‘read Right Multipurpose education society’ suka saba shiryawa.

ADVERTISEMENT

Daliban da suka fafata acikin wannan gasa sun hada da dalibai 41 daga karamar sikandire da dalibai 54 daga babar sikandire sai dalibai 19 masu karatun digiri da kuma mutum biyu masu karatun digiri na biyu.

Daga cikin mahimman batutuwa da aka gudanar da wannan gasar ta bana sun hada da batun samar da tsaftattaccen ruwa sha da daidaito akan batun macce da Namiji da wakoki akan irin rawar da mata ke takawa wajan samar da tsaftattaccen ruwan sha da batun ciwon daji ‘cancer’ da dai sauransu
Haka kuma kowanne rikuni an fitar na daya zuwa na uku inda aka basu kyaututtuka da kudadai domin kara masu kwarin gwiwa musamman abinda ya shafi karatun su.

LABARAI MASU NASABA

Goron Juma’a

GORON JUMA’A 22-05-2026

Da take gabatar da jawabi, uwargidan Gwamnan Jihar Katsina, Hajiya Fatima Dikko Umar Radda ta nuna farin cikinta a kan yadda dalibai suka nuna kwazo da jajircewa a lokacin wannan gasa da ta gudana.

Hajiya Fatima Dikko Radda na mai cewa hakika kun zama abin alfahari ga al’ummar Jihar Katsina ta yadda da irin haka ne za ku canza alkiblar ilimi musamman na ‘ya’ya mata a jihar Katsina da arewacin Nijeriya.

Ta kuma kara da cewa shirya irin wannan gasa zai kara wa sauran mata kwarin gwiwa domin su tashi tsaye wajan ganin an yi gogayya da wasu ta fannin ilimi da sauran bangarori.

“A yau nake kara tabbatarwa cewa ilimin ‘ya ‘ya mata abu ne da ke da matukar muhimmanci a rayuwar duniya da lahira saboda haka ina kara kira ga iyaye da malamai da masu ruwa da tsaki a kan sha’anin ilimi da mu kara ba da himma wajan samar da sabuwar al’umma mai dauke da tarin ilimi da zamani da na addini” in ji ta.

Tunda farko shugabar kungiyar ‘Read Right Multipurpose education society’ Aliyu Nasir Kankara ya bayyana wasu ayyukan wannan kungiyar inda ya ce an samu gagarumar nasara a cikin wannan shekarar ta 2023.

“Mun kaddamar da rabon littattafai a karamar hukumar Musawa da Dabai a karamar hukumar Danja, mun yi gangamin wayar da kai akan sha’anin shugabanci da kuma bayar da abinci a lokacin wata Ramadan din da ya gabata”. In ji shi.

Ya kara da cewa a shirin su na a koma makaranta ”Back to School Campaign’ sun samu nasarar dawowa da yaran da ba sa zuwa makaranta 7,500, sannan sun yi taron wayar da kai dangane da matsalar rikice-rikecen cikin gida da sauran batutuwa da suka shafi al’umma.

Ita ma a nata jawabin kwamishiniyar ilimi a matakin farko da babar sikandire Hajiya Hadiza Yar’adua ta yi bayanin cewa irin wannan gasa na nuna irin yadda aka nuna kulawa ga ilimin ‘ya ‘ya mata.

Ta ce ko ba komi an sanar da wata sabuwar hanya ta karfafa gwiwar ‘ya ‘ya mata wanda hakan ba zai sa a bar su a baya ba ta bangarori da dama.

” Yanzu muryoyin ‘ya ‘ya mata za su fara yin amo na gaskiya musamman abubuwan da suka shafi ilimi na zamani da kuma na addini” in ji ta.

Kazalika ita da take nata ta’aliki, kwamishiniyar harkokin mata ta jihar Katsina Hajiya Zainab Musa Musawa ta nuna mahimmancin yin ilimin ga ‘ya ‘ya mata musamman a wannan lokaci da ke da kalubale kala-kala na rayuwa.

Ta yi bayanin cewa ta ga mahimmancin yin ilimi wanda ta ce shi ne, tushe kuma ginshiki na kasancewarta a gaban wadannan dalibai tana yi masu jawabi, ta ce ba dan ilimi ba da sai dai wani abu ya hada su.

Bayan haka kwamishiniyar harkokin mata ta yi nuni cikin nishadi inda ta ce ” Bayan haka idan kuka duba mafiyawan matan da ke wannan baban tebur dukkan su ilimi ne ya kawo su wannan wuri.

An kammala wannan gasa ta adabi da bunkasa ilimi ‘ya ‘ya mata da aka kashe kwana biyu ana gudanarwa a Katsina tare da raba kyaututtuka ga wadanda suka samu nasara lashe gasar.

Matar Gwamnan Katsina
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina

MASU ALAKA

GORON JUMA’A 17-04-2026
Goron Juma'a

Goron Juma’a

June 5, 2026
GORON JUMA’A 01-07-2025
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 22-05-2026

May 22, 2026
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025
Labarai

Ku Kula Da Kyawawan Ɗabi’u, Su Ne Waɗanda Annabi SAW Ya Kira Duk Halitta A Kansu

April 17, 2026
Next Post
Shigar Mutunci

Koya Wa Yara Shigar Mutunci (I)

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026
Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

July 5, 2026
Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.