• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iyaye Mu Kara Himmar Samar Da Al’umma Mai Tarin Ilimi –Matar Gwamnan Katsina

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Al'adu
0
Matar Gwamnan katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gudanar da gasar adabi domin bunkasa ilimin ‘ya ‘ya mata karo na uku mai taken ‘Fatima Dikko Radda girls child education summit and literacy contest’.

Ita dai wannan gasa na da nufin karfafa gwiwar ‘ya ‘ya mata musamman abinda ya shafi karatun su tun daga matakin firamare har zuwa jami’a ta yadda za su rika samun wakilci a duk sauran al’amura.

  • Gwamna Radda Ya Yi Allah Wadai Da Hare-haren ‘Yan Fashin Daji A Jihar Katsina 
  • Yadda Mahara Suka Kashe Mutane Da Sace Wasu Da Dama A Wurin Maulidi A Katsina

A karo na uku na wannan gasa, an zakulo dalibai daga bangarori hudu da suka hada da karamar sikadara da babar sikadare da masu digiri da kuma masu digiri na biyu domin fafatawa a wannan gasa wanda kungiyar ‘read Right Multipurpose education society’ suka saba shiryawa.

Daliban da suka fafata acikin wannan gasa sun hada da dalibai 41 daga karamar sikandire da dalibai 54 daga babar sikandire sai dalibai 19 masu karatun digiri da kuma mutum biyu masu karatun digiri na biyu.

Daga cikin mahimman batutuwa da aka gudanar da wannan gasar ta bana sun hada da batun samar da tsaftattaccen ruwa sha da daidaito akan batun macce da Namiji da wakoki akan irin rawar da mata ke takawa wajan samar da tsaftattaccen ruwan sha da batun ciwon daji ‘cancer’ da dai sauransu
Haka kuma kowanne rikuni an fitar na daya zuwa na uku inda aka basu kyaututtuka da kudadai domin kara masu kwarin gwiwa musamman abinda ya shafi karatun su.

Labarai Masu Nasaba

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

GORON JUMA’A 20-06-2025

Da take gabatar da jawabi, uwargidan Gwamnan Jihar Katsina, Hajiya Fatima Dikko Umar Radda ta nuna farin cikinta a kan yadda dalibai suka nuna kwazo da jajircewa a lokacin wannan gasa da ta gudana.

Hajiya Fatima Dikko Radda na mai cewa hakika kun zama abin alfahari ga al’ummar Jihar Katsina ta yadda da irin haka ne za ku canza alkiblar ilimi musamman na ‘ya’ya mata a jihar Katsina da arewacin Nijeriya.

Ta kuma kara da cewa shirya irin wannan gasa zai kara wa sauran mata kwarin gwiwa domin su tashi tsaye wajan ganin an yi gogayya da wasu ta fannin ilimi da sauran bangarori.

“A yau nake kara tabbatarwa cewa ilimin ‘ya ‘ya mata abu ne da ke da matukar muhimmanci a rayuwar duniya da lahira saboda haka ina kara kira ga iyaye da malamai da masu ruwa da tsaki a kan sha’anin ilimi da mu kara ba da himma wajan samar da sabuwar al’umma mai dauke da tarin ilimi da zamani da na addini” in ji ta.

Tunda farko shugabar kungiyar ‘Read Right Multipurpose education society’ Aliyu Nasir Kankara ya bayyana wasu ayyukan wannan kungiyar inda ya ce an samu gagarumar nasara a cikin wannan shekarar ta 2023.

“Mun kaddamar da rabon littattafai a karamar hukumar Musawa da Dabai a karamar hukumar Danja, mun yi gangamin wayar da kai akan sha’anin shugabanci da kuma bayar da abinci a lokacin wata Ramadan din da ya gabata”. In ji shi.

Ya kara da cewa a shirin su na a koma makaranta ”Back to School Campaign’ sun samu nasarar dawowa da yaran da ba sa zuwa makaranta 7,500, sannan sun yi taron wayar da kai dangane da matsalar rikice-rikecen cikin gida da sauran batutuwa da suka shafi al’umma.

Ita ma a nata jawabin kwamishiniyar ilimi a matakin farko da babar sikandire Hajiya Hadiza Yar’adua ta yi bayanin cewa irin wannan gasa na nuna irin yadda aka nuna kulawa ga ilimin ‘ya ‘ya mata.

Ta ce ko ba komi an sanar da wata sabuwar hanya ta karfafa gwiwar ‘ya ‘ya mata wanda hakan ba zai sa a bar su a baya ba ta bangarori da dama.

” Yanzu muryoyin ‘ya ‘ya mata za su fara yin amo na gaskiya musamman abubuwan da suka shafi ilimi na zamani da kuma na addini” in ji ta.

Kazalika ita da take nata ta’aliki, kwamishiniyar harkokin mata ta jihar Katsina Hajiya Zainab Musa Musawa ta nuna mahimmancin yin ilimin ga ‘ya ‘ya mata musamman a wannan lokaci da ke da kalubale kala-kala na rayuwa.

Ta yi bayanin cewa ta ga mahimmancin yin ilimi wanda ta ce shi ne, tushe kuma ginshiki na kasancewarta a gaban wadannan dalibai tana yi masu jawabi, ta ce ba dan ilimi ba da sai dai wani abu ya hada su.

Bayan haka kwamishiniyar harkokin mata ta yi nuni cikin nishadi inda ta ce ” Bayan haka idan kuka duba mafiyawan matan da ke wannan baban tebur dukkan su ilimi ne ya kawo su wannan wuri.

An kammala wannan gasa ta adabi da bunkasa ilimi ‘ya ‘ya mata da aka kashe kwana biyu ana gudanarwa a Katsina tare da raba kyaututtuka ga wadanda suka samu nasara lashe gasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dikko RaddaFatima RaddaKungiyar matar gwamnoni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yaushe Za A Fara Kofin Duniya Na Kungiyoyi?

Next Post

Koya Wa Yara Shigar Mutunci (I)

Related

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya
Goron Juma'a

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

7 days ago
GORON JUMA’A 16/05/2025
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 20-06-2025

2 weeks ago
Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana
Al'adu

Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

4 weeks ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 30-03-2025

1 month ago
GORON JUMA’A 16/05/2025
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 16/05/2025

2 months ago
GORON JUMA’A
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 28-03-2025

3 months ago
Next Post
Shigar Mutunci

Koya Wa Yara Shigar Mutunci (I)

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.