Jama’a barkanku da wannan rana ta juma’a, barkanku da kasancewa tare da wannan shafi na GORON JUMA’A, shafin da yake bawa kowa damar miƙa saƙon gaishe-gaishensa zuwa ga ƴan’uwa da abokan arziƙi, na kusa da na nesa, har ma da waɗanda aka daɗe ba a haɗu ba.
Kamar kowane mako yau ma shafin na tafe da wasu saƙonnin gaishe-gaishen da ku ka aiko mana, amma za mu fara miƙa gaisuwar mu ga Babban Editanmu Alhaji Bello Hamza. saƙon farko ya fara da cewa:
Saƙo daga Fatiyya Jibril Isah Jihar Kaduna:
Ina gaida Uwar ɗakina kuma Uwata a gurin Sana’a wato Hajiyya Aisha Mai abinci. Sannan ƙawata kuma aminiyata wato Shamsiyya, sai ƴan’uwana na gida kamar su Hajja Uwani mai Alala, sai Mardiyya, Zulai da dai sauransu. Sai ƴan’uwana dake Kano da Maiduguri da fatan sun yi sallar juma’a lafiya.
Saƙo daga Hamisu Bala Dagaci daga Jihar Kano:
Da farko ina miƙa saƙon goron juma’ata zuwa ga ɗaukacin jama’a musulmi barka da juma’a, sai ƴan’uwana na kusa da na nesa da abokan arziƙi, maƙofta da dai sauransu kamar Alhaji Mamman Shitu, Yusha’u Garba Danlami, Jamilu Mahummad.
Sunana Fatima Mustapha Hashim daga Jihar Zamfara:
Ina gaida Mamana da Baffana, sai yayata dake garin Maiduguri wato Yaya Hajiya, sai Yaya Mu’azu dayake karatu a Katsina. Sai ƙawayena na makaranta Suwaibah Muhammad, Hajara, Zauwariyya, Zaina Abdulmajeed, Rukayya Abdullahi, Kausar Nuhu, Fatima Suleiman, Aisha Hafizu, da dai sauransu. Da fatan sun yi juma’a lafiyya, Amin.
Saƙo daga Maimunatu Aliyu Minjibir jihar Kano:
Ina gaida Mahaifiyata da Mahaifina, Hajiya Saratu da Alhaji Aliyu Minjibir. Sai Gidana Alhaji Musa Yusuf, sai aminiyata Hajiya Kubra Bashir Abdullahi, sai ƴata Mariya, da ƙannena Rashida Aliyu Minjibir, Zainab Aliyu Minjibir, Aliya Aliyu Minjibir, Aliyu Aliyu, Abubakar Aliyu Minjibir Muhammad Aliyu Minjibir, da fatan sun yi juma’a lafiya.














Discussion about this post